Thursday, 31 March 2022

An Karɓo Daga Abi-Hurairah (ra) Yace


An Karɓo Daga Abi-Hurairah (ra) Yace: Manzon Allah (ﷺ) Yaga Wani Mutum Kwance Akan Cikinsa, Sai Yace Dashi: “Lallai Wannan Kwanciya Ce Da Allah Baya Sonta".
(Tirmizi Ya Ruwaitoshi)

A Ruwayar Bukhari Kuma Manzon Allah (ﷺ) Cewa Yayi:
(إِنَّمَا هَذِهِ ضِجْعَةُ أَهْلِ النَّارِ)

“Lallai Wannan Kwanciya Ce Ta Ƴan Wuta".

*6. RUFE ƘOFOFI DA KASHI FITILU DA KAFIN KWANCIYA BACCI:*
Yana Daga Cikin Ladubban Kwanciya Mutum Ya Rufe Ƙofar Gida da Ƙofar Ɗaki. Sannan Ka Fitilun dake Ɗakin, Sannan a Rufe Abinci da Duk Abin Sha. Hadisi Ya Tabbata Manzon Allah (ﷺ) Yana Cewa:
عَنْ جَابِرٍ قَالَ: قَالَ رَسُولُ اللَّهِ صَلَّى اللَّهُ عَلَيْهِ وَسَلَّمَ-: (أَطْفِئُوا الْمَصَابِيحَ بِاللَّيْلِ إِذَا رَقَدْتُمْ، وَغَلِّقُوا الأَبْوَابَ، وَخَمِّرُوا الطَّعَامَ وَالشَّرَابَ)
 (روا لبخاري)

An Kar6o Daga Jabir (ra) Yace: Manzon Allah (ﷺ) Yace: “Ku Kashe Fitilu Yayin da Kuka Tashi Yin Bacci. Kuma Ku Kukkule Ƙofofinku, Ku Rufe Abinci Da Abin Sha".
(Bukhari Ya Ruwaitoshi)

DAGA CIKIN LADUBBAN KWANCIYA BACCI (04)

        Da Sunan Allah Mai Rahma Mai Jinƙai

*7. YIN ADDU'OI:*
 Bayan Mutum Ya Rufe Ƙofofi da Kashe Fitilu, Ladabi Na Gama Shine Yin Addu'a Bayan Ka Kwanta ta 6angaren Jikinka Na Dama. Akwai Addu'oi Masu Yawa da Ya Tabbata Daga Manzon Allah (ﷺ) Na Karantawa. Kaɗan Daga Cikinsu Sun Haɗa da:

١. اللَّهُ لَا إِلَٰهَ إِلَّا هُوَ الْحَيُّ الْقَيُّومُ ۚ لَا تَأْخُذُهُ سِنَةٌ وَلَا نَوْمٌ ۚ لَهُ مَا فِي السَّمَاوَاتِ وَمَا فِي الْأَرْضِ ۗ مَنْ ذَا الَّذِي يَشْفَعُ عِنْدَهُ إِلَّا بِإِذْنِهِ ۚ يَعْلَمُ مَا بَيْنَ أَيْدِيهِمْ وَمَا خَلْفَهُمْ ۖ وَلَا يُحِيطُونَ بِشَيْءٍ مِنْ عِلْمِهِ إِلَّا بِمَا شَاءَ ۚ وَسِعَ كُرْسِيُّهُ السَّمَاوَاتِ وَالْأَرْضَ ۖ وَلَا يَئُودُهُ حِفْظُهُمَا ۚ وَهُوَ الْعَلِيُّ الْعَظِيمُ

٢. آمَنَ الرَّسُولُ بِمَا أُنزِلَ إِلَيْهِ مِن رَّبِّهِ وَالْمُؤْمِنُونَ ۚ كُلٌّ آمَنَ بِاللَّهِ وَمَلَائِكَتِهِ وَكُتُبِهِ وَرُسُلِهِ لَا نُفَرِّقُ بَيْنَ أَحَدٍ مِّن رُّسُلِهِ ۚ وَقَالُوا سَمِعْنَا وَأَطَعْنَا ۖ غُفْرَانَكَ رَبَّنَا وَإِلَيْكَ الْمَصِيرُ 
 ۝ (٢٨٥) لَا يُكَلِّفُ اللَّهُ نَفْسًا إِلَّا وُسْعَهَا ۚ لَهَا مَا كَسَبَتْ وَعَلَيْهَا مَا اكْتَسَبَتْ ۗ رَبَّنَا لَا تُؤَاخِذْنَا إِن نَّسِينَا أَوْ أَخْطَأْنَا ۚ رَبَّنَا وَلَا تَحْمِلْ عَلَيْنَا إِصْرًا كَمَا حَمَلْتَهُ عَلَى الَّذِينَ مِن قَبْلِنَا ۚ رَبَّنَا وَلَا تُحَمِّلْنَا مَا لَا طَاقَةَ لَنَا بِهِ ۖ وَاعْفُ عَنَّا وَاغْفِرْ لَنَا وَارْحَمْنَا ۚ أَنتَ مَوْلَانَا فَانصُرْنَا عَلَى الْقَوْمِ الْكَافِرِينَ

٣. ﺑﺴﻢ ﺍﻟﻠﻪ ﺍﻟﺮﺣﻤﻦ ﺍﻟﺮﺣﻴﻢ ﻗُﻞْ ﻫُﻮَ ﺍﻟﻠَّﻪُ ﺃَﺣَﺪٌ  ۝ ﺍﻟﻠَّﻪُ ﺍﻟﺼَّﻤَﺪُ ۝ ﻟَﻢْ ﻳَﻠِﺪْ ﻭَﻟَﻢْ ﻳُﻮﻟَﺪْ  ۝ ﻭَﻟَﻢْ ﻳَﻜُﻦْ ﻟَﻪُ ﻛُﻔُﻮًﺍ ﺃَﺣَﺪٌ ۝ 

٤. قُلْ أَعُوذُ بِرَبِّ الْفَلَقِ ۝ مِنْ شَرِّ مَا خَلَقَ ۝ وَمِنْ شَرِّ غَاسِقٍ إِذَا وَقَبَ ۝ وَمِنْ شَرِّ النَّفَّاثَاتِ فِي الْعُقَدِ ۝ وَمِنْ شَرِّ حَاسِدٍ إِذَا حَسَدَ ۝

٥. قُلْ أَعُوذُ بِرَبِّ النَّاسِ ۝ مَلِكِ النَّاسِ ۝ إِلَهِ النَّاسِ ۝ مِنْ شَرِّ الْوَسْوَاسِ الْخَنَّاسِ ۝ الَّذِي يُوَسْوِسُ فِي صُدُورِ النَّاسِ ۝ مِنَ الْجِنَّةِ وَالنَّاسِ ۝

٦. قُلْ يَا أَيُّهَا الْكَافِرُونَ ۝ لَا أَعْبُدُ مَا تَعْبُدُونَ ۝ وَلَا أَنْتُمْ عَابِدُونَ مَا أَعْبُدُ ۝ وَلَا أَنَا عَابِدٌ مَا عَبَدْتُمْ ۝ وَلَا أَنْتُمْ عَابِدُونَ مَا أَعْبُدُ ۝ لَكُمْ دِينُكُمْ وَلِيَ دِينِ ۝

٧. اللَّهُمَّ قِني عَذَابَكَ يَوْمَ تَبْعَثُ عِبَادَكَ

٨. بِاسْمِكَ اللَّهُمَّ أَمُوتُ وَأَحْيَا

٩. بِاسمِكَ رَبي وَضَعتُ جَنبِي، وبِكَ أَرفَعُهُ، إِن أَمسَكتَ نَفسِي فارحَمها وإِن أَرسَلتَها فاحفَظها بِما تَحفَظُ بِهِ عِبَادَكَ الصالِحينَ"

*8. YIN ADDU'A YAYIN FARKAWA CIKIN BACCI:*
 Mustahabi ne Idan Mutum Ya Farka Cikin Dare Yayin da Yake Bacci Ya Ambaci Ubangijinsa da Wannan Addu'ar:
(أَعُوذُ بِكَلِمَاتِ اللهِ التَّامَّةِ مِنْ غَضَبِهِ وَعِقَابِهِ ، وَشَرِّ عِبَادِهِ ، وَمَنْ هَمَزَاتِ الشَّيَاطِينِ)

“A'UZU BI KALIMÃTULLAHIT TAMMÃT MIN GHADABIHI WA IQÃBIHI, WA SHARRI IBÃDIHI, WAMIN HAMAZÃTISH SHAYÃƊIN".

ALLAH KA TSARE DAGA SHARRIN MUTUM DA ALJANI. MASU NUFIN MU DA SHARRI KA MAYAR MUSU DA SHARRINSU

سُبْحَانَكَ اللَّهُمَّ وَبِحَمْدِكَ، أَشْهَدُ أَنْ لا إِلَهَ إِلا أَنْتَ، أَسْتَغْفِرُكَ وَأَتُوبُ إِلَيْكَ











Taskar asirai malam tv AL falaki tv Ramli da hisabi tv Mafarkinka sirrinka tv Gudun duniya tv Domin Karin bayani Sai a turo SAKO ta nombarmu ko email zamu baku amsa 👇🤳 taskaasirai@gmail.com 08124763287 08144698283

Wednesday, 30 March 2022

TSARABAR RAMADAN DOMIN SAMUN KUDIN HIDIMAR AZUMI DA SALLAH

SALLAR TUBA GA ALLAH





SALLAR TUBA GA ALLAH

An ruwaito daga Abubakar Assiddeeq (RA) ya ce: Na ji Manzon Allah (SAW) yana cewa: "Babu wani bawa da zai aikata wani zunubi, sai ya kyautata alwala, sannan ya tashi ya yi sallah raka'a biyu, sai ya roki gafaran Allah face Allah ya gafarta masa, sannan ya karanta wannan Ayar: "Kuma waɗanda suke idan suka aikata wata alfãsha ko suka zãlunci kansu sai su tunã da Allah, sai su nẽmi gãfarar zunubansu ga Allah. Kuma wãne ne ke gãfara ga zunubai, fãce Allah? Kuma ba su dõge a kan abin da suka aikata ba, alhãli kuwa suna sane". 
Abu Dawud ya ruwaito, Albaniy ya ingantashi.

💦

Yana daga cikin rahamar Allah ga bayinsa bude kofar tuba a garesu wacce ba ta yankewa har sai in an zo gargarar mutuwa ko idan rana ta fito daga mafadarta.

Sababin wannan sallar shine: idan mutum ya fada cikin zunubi babba ko karama, to lallai yana wajaba a gareshi da ya gaggauta tuba ga Allah, bayan nan an so yayi wannan raka'oi guda biyu, wato mutum ya aikata wani aikin da'a don samun kusanci ga Allah, yayi tawassuli da ita ga Allah yana mai fata da kwadayin Allah ya karbi tubansa ya gafarta masa zunubansa.

●LOKACIN YIN TA:

Mustahabbi ne yin wannan sallah a lokacin da mutum yayi azamar tuba daga zunubin da ya aikata, nan take ne yayi zunubin ko kuwa an dauki lokaci da ya aikata zunubin, Ita wannan sallah an shar'anta yin ta a kowane lokaci har a lokutan da a ka hana yin nafila, saboda ita sallah ce da take da sababi, don haka an shar'anta ta duk a ka samu sababinta.

●SIFAR SALLAR TUBA

•Sallah ce nafila raka'a biyu.
•Mutum zai sallace ta shi kadai ba a jam'i ba.
•Mutum zai karanta abin da ya sawwaka mishi na daga Alkur'ani.

●Mutahabbi ne ga wanda ya tuba daga wani zunubi to ya dage da aikata ayyuka na kwarai, saboda fadin Allah:

"وَإِنِّي لَغَفَّارٌ لِّمَن تَابَ وَآمَنَ وَعَمِلَ صَالِحًا ثُمَّ اهْتَدَىٰ". (طـه :82) 

"Kuma lalle Nĩ haƙĩƙa Mai gãfara ne ga wanda ya tũba kuma ya yi ĩmãni, kuma ya aikata aikin ƙwarai, sa'an nan kuma ya nẽmi shiryuwa".

●Mafi falalar wadannan ayyuka da mai tuba zai yi shi ne: SADAKA, domin sadaka tana daga cikin manyan sabubban da suke kankare zunubai, Allah Madaukaki ya ce:

"إِن تُبْدُوا الصَّدَقَاتِ فَنِعِمَّا هِيَ ۖ وَإِن تُخْفُوهَا وَتُؤْتُوهَا الْفُقَرَاءَ فَهُوَ خَيْرٌ لَّكُمْ ۚ وَيُكَفِّرُ عَنكُم مِّن سَيِّئَاتِكُمْ ۗ وَاللَّهُ بِمَا تَعْمَلُونَ خَبِيرٌ"
(البقرة :271) 

"Idan kun bayyana sadakõki to, yana da kyau ƙwarai kuma idan kuka ɓõye su kuma kuka je da su ga matalauta, to shi ne mafi alhẽri a gareku, kuma Yana kankarẽwa daga barinku daga miyãgun ayyukanku. Kuma Allah ga abin da kuke aikatawa Masani ne".

Kuma ya tabbata a hadisin Ka'ab bn Malik (RA) cewa, a lokacin da Allah ya karba tubansa ya ce: Ya Manzon Allah yana daga cikin cikan tubana in bayar da dukiyata sadaka ga Allah da Manzonsa, sai Manzon Allah (SAW) ya ce: ka rike wani yanki na dukiyarka don alkhairi ne a gareka...". Muttafakun alaihi.

Allah ya azurtamu da yin ingantacciyar tuba, tuban da ba za mu sake komawa ga wannan zunubin ba.












Taskar asirai malam tv AL falaki tv Ramli da hisabi tv Mafarkinka sirrinka tv Gudun duniya tv Domin Karin bayani Sai a turo SAKO ta nombarmu ko email zamu baku amsa 👇🤳 taskaasirai@gmail.com 08124763287 08144698283

_MANYAN ILLOLI GUDA SHIDA NA SABAWA MAHAIFA_*


_MANYAN ILLOLI GUDA SHIDA NA SABAWA MAHAIFA_*


Hakika Annabi SAW ya yi mana umarni kamar yadda Allah da kansa yayi mana umarnin akan yin biyayya da kuma kyautata mahaifa,da kuma hani akan sabawa masu da kuma cutar dasu,sabawa mahaifa da rashin kyautata masu yana cikin mafi girma zunubai da akewa yiwa Allah anan duniya.


Annabi SAW ya baiyana mana illa da girman laifin mai sabawa Mahaifansa, ga kadan daga cikin su:-


1-ILLA TA FARKO

*Mai Cutar da mahaifansa Tsinanne ne inji Manzon Allah SAW*.


Daga Abu Hurairaita R.A yana cewa :-

"Annabi s.a.w yana cewa:-

*(La'antacce ne mai cutar da mahaifansa ko mai sabawa mahaifansa)*

@ﺍﻟﻄﺒﺮﺍﻧﻲ ﻓﻲ" ﺍﻷﻭﺳﻂ

" ‏( 8497 ‏)

@ﻭﺻﺤﺤﻪ ﺍﻷﻟﺒﺎﻧﻲ ﻓﻲ " ﺻﺤﻴﺢ ﺍﻟﺘﺮﻏﻴﺐ " ‏( 2420 ‏)


2-ILLA TA BIYU

*Allah bawa kallon mai sabawa Mahaifansa a ranar alqiyama*.


Daga Ibn Umar R.A yana cewa:-

" Manzon Allah s.a.w yace:

(Mutane guda ukku Allah bazai kallesu ba a ranar alqiyama:-

*Mai sabawa mahaifansa*

*Wanda baya kishin iyalinsa

...............)*.

@ﻭﺭﻭﻯ ﺍﻟﻨﺴﺎﺋﻲ ‏( 2562 ‏)

@ﻭﺻﺤﺤﻪ ﺍﻷﻟﺒﺎﻧﻲ ﻓﻲ " ﺻﺤﻴﺢ

ﺳﻨﻦ ﺍﻟﻨﺴﺎﺋﻲ


3-ILLA TA UKKU

*Mai sabwa mahaifa baya shiga aljanna*.


Daga Ibn Umar R.A yana cewa:-

" Manzon Allah s.a.w yace:

(..............Mutane guda ukku bazasu shiga aljanna ba a gobe alqiyama:-

*Mai sabawa mahaifansa*

*Mai kwankwadar giya*

*Mai yin gorin abinda ya bada)*. 

@ﻭﺭﻭﻯ ﺍﻟﻨﺴﺎﺋﻲ ‏( 2562 ‏)

@ﻭﺻﺤﺤﻪ ﺍﻷﻟﺒﺎﻧﻲ ﻓﻲ " ﺻﺤﻴﺢ

ﺳﻨﻦ ﺍﻟﻨﺴﺎﺋﻲ " .


4-ILLA TA HUDU

*Babu mai shiga aljanna sai wanda kasance yana biyayya ga mahaifansa kuma baya saba masu*.


Wani mutum yazo wajan Annabi s.a.w sai yace Ya Manzon Allah s.a.w:

"Na shaida babu abin bautawa bisa hakki da gaskiya sao Allah kuma kai Manzon Allah ne, kuma nayi salloli biyar na farilla,kuma na bada zakka kuma nayi azumin watan Ramada?? Sai Annabi s.a.w ya ce:

*(Wanda ya mutum akan haka yana tare da Annabawa da Shahidai Siddiqai a ranar alqiyama matuqar bai sabawa Mahaifansa ba)*

@ﻭﺭﻭﻯ ﺃﺣﻤﺪ ‏(24299 ‏)

@ﻭﺻﺤﺤﻪ ﺍﻷﻟﺒﺎﻧﻲ ﻓﻲ " ﺻﺤﻴﺢ ﺍﻟﺘﺮﻏﻴﺐ " ‏( 2515 ‏)


5-ILLA TA BIYAR

*Allah baya karbar aiyuka na mai sabawa mahaifansa inji Manzon Allah s.a.w*.


Daga Abi Umamah R.A yana cewa:

Manzon Allah s.a.w yace:

(Mutanan guda ukku Allah baya karbar aiyukan su na farilla da na nafila:-

*Mai sabawa Mahaifansa*

*Mai gorin abinda ya bayar*

*Wanda yake karyata Qaddara)*.

@ﺭﻭﺍﻩ ﺍﺑﻦ ﺃﺑﻲ ﻋﺎﺻﻢ ﻓﻲ "

ﺍﻟﺴﻨﺔ " ‏( 323 ‏) 

@ﺳﻠﺴﻠﺔ ﺍﻷﺣﺎﺩﻳﺚ ﺍﻟﺼﺤﻴﺤﺔ " ‏( 1785 ‏) ،


6-ILLA TA SHIDA

*Sabawa mahaifa yana cikin mafi giraman zunubai inji Annabi s.a.w*.


(ﺃﻻ ﺃﻧﺒﺌﻜﻢ ﺑﺄﻛﺒﺮ ﺍﻟﻜﺒﺎﺋﺮ ؟ ﻗﻠﻨﺎ : ﺑﻠﻰ ﻳﺎ ﺭﺳﻮﻝ ﺍﻟﻠﻪ ؟ ﻗﺎﻝ : ﺍﻹﺷﺮﺍﻙ ﺑﺎﻟﻠﻪ ﻭﻋﻘﻮﻕ ﺍﻟﻮﺍﻟﺪﻳﻦ . ﻭﻛﺎﻥ ﻣﺘﻜﺌﺎً ﻓﺠﻠﺲ ، ﻭﻗﺎﻝ : ﺃﻻ ﻭﻗﻮﻝ ﺍﻟﺰﻭﺭ. ﺃﻻ ﻭﺷﻬﺎﺩﺓ ﺍﻟﺰﻭﺭ ‏) ﻣﺘﻔﻖ ﻋﻠﻰ ﺻﺤﺘﻪ.


Allah ka nisantar da mu daga aikata abinda zai sanya mu sabawa Mahaifanmu.


Allah ka jikansu kamar yadda suka kulamu lokacin muna yara.


*Allah ka gafarta ma mahaifan mu baki daya*.














Taskar asirai malam tv AL falaki tv Ramli da hisabi tv Mafarkinka sirrinka tv Gudun duniya tv Domin Karin bayani Sai a turo SAKO ta nombarmu ko email zamu baku amsa 👇🤳 taskaasirai@gmail.com 08124763287 08144698283

Tuesday, 29 March 2022

*SHAN AZUMIN MAI CIKI DA MAI JEGO: RAMUWA KO CIYARWA?*

*SHAN AZUMIN MAI CIKI DA MAI JEGO: RAMUWA KO CIYARWA?*
.
.
Abu na farko da ya kamata a sani cewa, ba ya halasta ga mai ciki ko mai jego ta sha azumi don kawai tana da juna biyu ko tana shayar da jariri. Sai dai in akwai tsoron cewa azumi zai iya cutar da lafiyarta ko ya jawo mata matsala ita kanta ko danta ko kuma su duka biyun. Idan ya tabbata cewa in ta yi azumi akwai matsala, to a lokacin ne ya halasta ta sha azumi.
Malamai sun yi sabani game da hukuncin mace mai ciki ko mai jego in ta sha azumi, shin ramawa za ta yi ko ciyarwa ko kuma duka biyun? Akwai maganganu malamai kamar haka.
.
.
MAGANA TA FARKO
Abu Hanifah da Ibrahim Annakha’iy suna da ra’ayin cewa abin da ke kanta shine ramuwa kawai. Wannan kuma shine mazhabar Aliyu Dan Abu Dalib (Allah ya qara masa yarda).
MAGANA TA BIYU
In mace mai ciki ko mai shayarwa ta sha azumi saboda tana tsoron lafiyarta za ta rama ne kawai. In kuma ta sha ne saboda tsoron lafiyar danta da/ko abin da ke cikinta to za ta rama tare da ciyarwa. Wannan ita ce maganar Maliku da Sufyan da Shafi’iy da Ahmad Bn Hanbal. Hakanan kuma Al-Jassas ya hakaito irin wannan fatawa daga Abdullahi Dan Umar (Allah ya qara musu yarda) Haka nan ma Maliku ya hakaito a Muwadda daga Ibn Umar din.
 .
.
MAGANA TA UKU
In mace mai ciki ko mai shayarwa ta sha azumi abin da ke kanta shine ciyarwa kawai, babu ramuwa. Ibn Abbas (Allah ya qara musu yarda) shine ke da wannan ra’ayin cikin sahabbai. Haka nan kuma Ibn Qudamah ya hakaito irin wannan magana daga Ibn Umar (Allah ya qara musu yarda).
MAGANA TA HUDU
Mai shayarwa in ta ji tsoro saboda jaririnta to za ta sha ruwa sai ta ciyar. Mai ciki kuma in ta sha za ta rama ne; domin ta fi kama da maras lafiya. Wannan shine mazhabin Alhasan Albasariy.
 .
.
MAGANA TA BIYAR
Idan mai ciki ko mai jego ta sha azumi to ciyarwa ne akanta ba bu ramuwa, amma tana da zabin ta rama ba tare da ciyarwa ba. Wannan ita ce maganar Ishaq Dan Rahwuya.

Almubarakfuriy ya naqalto maganar Ibn Hajrin a inda yake cewa: “An yi sabani game da mai ciki da mai shayarwa da kuma wanda ya sha azumi saboda tsufa in ya sami qarshin ramawa daga baya. Shafi’iy ya ce: za su rama kuma su ciyar, Auza’iy da mutanen Kufa suka ce ramuwa ce kawai akan su banda ciyarwa”. Sa’annan ya ambaci maganganun malamai mabambamta sannan ya ce: “Abin da ya bayyana gare ni shine cewa mai ciki da mai shayarwa suna daukan hukuncin maras lafiya ne da matafiyi. Allah shine mafi sani”.

Haka nan Ibn Qudama ya hakaito maganganun malamai da hujjojin su akan mas’alar sannan ya tabbatar da cewa abin da yake ganin shine daidai shine ramuwa ce akan matar da ta ji tsoro don kan ta, da kuma ramuwa da ciyarwa a kan wacce ta ji tsoro saboda kan ta da kuma yaronta.
Ibn Bazz ya fadi cewa: “da mai ciki da mai shayarwa [in sun sha azumi] hukuncinsu shine irin hukuncin maras lafiya. Saboda haka in sun kasa yin azumi za su rama daga baya. Wasu malamai kuma sun tafi izuwa ga cewa ciyarwa za su yi, amma wannan magana ce mai rauni. Abin da yake daidai shine ramuwa ce akan su kamar yadda take kan maras lafiya da matafiyi idan sun sha azumi”. Sannan ya kara cewa: “abin da yake daidai shine mai ciki da mai jego in sun sha azumi su rama. Abin da aka ruwaito daga Ibn Abbas na cewa ciyarwa ce kawai a kansu wannan zance ne mai rauni kuma ya saba wa dalilai na shari’a…”.

A cikin fatawar majalisar qoli ta malaman kasar Saudia sun ce: “In mace mai ciki ko mai sharyarwa ta ji tsoron abin da zai faru gare ta ko ga dan ta sai ta sha azumi to ramuwa ne akan ta, hukuncin daya ne da hukuncin maras lafiya wanda ya kasa yin azumi saboda tsoron cutarwa ga kansa. Allah ya ce: (Kuma wanda daga cikinku ya kasace ba shi da lafiya ko kuma yana halin tafiya [in ya sha azumi] to ya rama adadin kwanakin da ya sha daga baya [Baqara, 185])”. Sannan suka sake cewa: “Ita kuwa mai ciki, ya wajaba akan ta tai azumi sai dai in ta ji tsoron cewa azumin zai cutar da ita ko ya cutar da abin da ke cikinta, to anan an yi mata rangwame ta sha azumi, sannan ta rama bayan ta haihu ta kuma kuma tsarkaka daga jinin biqi….











Taskar asirai malam tv AL falaki tv Ramli da hisabi tv Mafarkinka sirrinka tv Gudun duniya tv Domin Karin bayani Sai a turo SAKO ta nombarmu ko email zamu baku amsa 👇🤳 taskaasirai@gmail.com 08124763287 08144698283

KUNDIN SIRRUKAN LI'ILAFI-QURAISHIN

Thursday, 24 March 2022

TASRIFIN ZOBE MAI FIDDA KUDI MANYA

MENE NE AZUMI...?? 1. AZUMI A LUGGA

 
MENE NE AZUMI...??

1. AZUMI A LUGGA
Shine kamewa
2. ASHARI'ANCE:- Shine kamewa daga barin chi ko sha da saduwa da iyali tun daga ketowar alfijir har zuwa faduwar rana da niyyar yin ibada.

RUKUNAN AZUMI

1. Yin niyya 

2. Kamewa dagachi ko sha da saduwa da iyali 
3. Zamani (lokachin yin azumi).

SUNNONIN AZUMI 
1. Gaggauta buda baki
2. Jinkirta sahur 
3. Addu'a yayin buda baki
4. Yin sahur da jinkirta shi.

MAKARUHAN AZUMI
1. Kaiwa matuka wajen kurkuran baki
2. Sumba
3. Dauwamar da kallo na sha' awa 
4. Tunani akan al'amuran saduwa
5. Shafa ko runguma 
6. Dandanan wani abu
7. Sanya tozali
8. Yin kaho.

ABUBUWAN DA SUKE BATA AZUMI
1. Saduwan wani abu zuwa makoshi (narkakke)
2. Fitarda maniyyi ko maziyyi da gangar
3. Saduwa ta hanyar tilasta
4. Chi ko sha da tunanin sauran dare
5. Chi ko sha da gangan
6. Saduwan wani abu wanda ba narkakkeba zuwa makoshi 
7. Ridda.

ABUBUWAN DA SUKE HALAS
1. Yin asiwaki
2. Sanyaya jiki da ruwa 
3. Tafiya ta halas
4. Sanya magani wanda ya dache
5. Tauna wani abu ga karamin yaro
6. Sanya turare.

ABUBUWAN DA AKAYI RANGWAME
1. Hadiye yawu
2. Rinjayen amai da magwas 
3. Rinjayen wani kwaro zuwa ga makoshi
4. Kuran kan hanya 
5. Wayan gari da janaba
6. Yin mafarki da rana

Ya kai dan uwa mai Albarka ka taya mu yada wannan karatu/sako zaka samu lada mai yawa, domin yada ilimi yana da daga cikin Abubuwan da suke kusan ta bawa ga Mahalicci.





Taskar asirai malam tv AL falaki tv Ramli da hisabi tv Mafarkinka sirrinka tv Gudun duniya tv Domin Karin bayani Sai a turo SAKO ta nombarmu ko email zamu baku amsa 👇🤳 taskaasirai@gmail.com 08124763287 08144698283

Wednesday, 23 March 2022

SAMUN IJABA TAKE

787
 .
Aslm bayin Allah masoya annabi S, a, w,
.
Ga alkawarin sirrin samun ijaba mai qarfi sosai 
.
.
Ranar lahadi ake farawa  har kwana 7
.
Ana rubuta شيجكذيش  kafa 777 idan aka wanke sai rubutun saika saka gaushi mai wuta acikin rubutun saika shanye take.. Saikayi wuridin.ya shaijakaziyshu.qafa 1000 to haka zakana yi  zuwa kwana, 7 to wllh idai kayi hakan  to insha allahu duk aikin dakayi zaka sami ijaba  cikin gaggawa mujarrabun sahihun  lashakka fiyhi
SIRRI





Taskar asirai malam tv AL falaki tv Ramli da hisabi tv Mafarkinka sirrinka tv Gudun duniya tv Domin Karin bayani Sai a turo SAKO ta nombarmu ko email zamu baku amsa 👇🤳 taskaasirai@gmail.com 08124763287 08144698283

Sunday, 20 March 2022

LABARI MAI GIRGIZA ZUCIYA

LABARI MAI GIRGIZA ZUCIYA


Abdullahi bn Almubarak (rah) yana daga cikin magabata na kwarai, kuma mutum ne Salihi. 

Wata shekara bayan yayi niyyar tafiya aikin Hajji, sai ya fita domin yin ban-kwana da abokansa (Almajiransa) kafin tafiyarsa. Amma akan hanyar ne yaga wani abu wanda ya tada masa hankali ya firgitashi. 

Ya hangi wata baiwar Allah tana tone juji (bola) tana tonowa wani MUSHEN KAZA wacce aka jefar. Ta daukota ta sanya a Qasan hammatarta, ta juya ta tafi aboye acikin duhu. 

Sai yayi kiranta yace "Mai kikeyi ya ke baiwar Allah?!". Sai tace "Ya kai bawan Allah,  kyale halittu da mahaliccinsu. Domin Allah yana da sha'ani acikin lamarin halittunsa".

Sai Ibnul Mubarak yace mata "Ina yi miki magiya don girman Allah ki gaya min labarinki".

Sai matar tace masa "Amma wallahi ba don ka riga kayi mun magiya ba, da ban gaya maka halin da nake ciki ba".

Kafin ta fara gaya masa har hawaye ya fara zuba daga idanunta. Sai tace "Hakika mu Allah ya halatta mana cin mushe. Domin ni Bazawara ce Matalauciya. Kuma (ni) mahaifiyar 'ya'ya mata ne guda huɗu".

"Mutuwa ta dauke Mahaifinsu mai kula dasu, Yanayi ya tsananta garemu, kuma dukiya ta Qare daga gareni. Kuma na kwankwasa kofofin mutane (wato na bibbi gidajen jama'a) amma ban samu wata zuciya mai tausayi daga wajensu ba".

"Sai na fita domin nemowa abinci ga 'Ya'yana wadanda wutar yunwa ta riga ta Qone musu hanta. Sai Allah ya azurtani da samun wannan mushen kazar da kake gani. Shin zakayi jayayya dani ne akanta?".

Daga jin wannan labari nan take sai Idanuwan Ibnul Mubarak suka rika zubda hawaye. Sai yace mata "Karbi wannan amanar". 

Sai ya damka mata dukkan dunkiyar da yayi niyyar tafiya aikin hajjin nan da ita. 

Sai Uwar marayun nan ta karba ta juya wajen 'ya'yanta tana godiya. Shi kuwa Ibnul Mubarak ya juya zuwa gidansa. Alhazai na garinsu kuma suka tafi suka sauke faralinsu sannan suka dawo. 

Amma abin mamakin duk da cewar shi bai je aikin Hajji ba, amma duk Alhazan sun dawo suna yin godiya gareshi bisa hidimar da yayi  musu awajen aikin Hajji. 

Suan cewa "Allah yaji Qanka Ya Kai Ibnul Mubarak! Babu wani wajen zama da muka zauna fache sai ka bamu wani abu daga ilimin da Allah ya sanar dakai. Kuma bamu ga wanda ya fika wajen bautarka ga Allah Ubangijinka ba, awajen aikin Hajjin nan na wannan shekarar".

Sai Ibnul Mubarak yayi mamaki kuma hankalinsa ya tashi game da al'amarinsa, da kuma al'amarinsu. Shi dai bai bar garinsa ba (ballantana ace har an ganshi awajen aikin Hajji). Kuma shi ba yaso ya bayyanar musu da sirrinsa. (wato ba yaso ya gaya musu cewar yayi sadaqah ne da kudinsa). 

To da ya kwanta barci sai yaga wani kyakkyawan mutum wanda haske ke fita daga fuskarsa. Yana ce masa "AMINCIN ALLAH YA TABBATA AGAREKA YA KAI ABDULLAHI. SHIN BAKA SAN KO NI WANENE BA? AI NINE MASOYIN NAN NAKA MUHAMMADUR RASULULLAHI (SAWW) NINE MASOYINKA ADUNIYA DA LAHIRA, KUMA NINE MAI CETONKA ARANAR LAHIRA. ALLAH YA SAKA MAKA DA ALKHAIRI BISA ABINDA KAYI MA AL'UMMATA".

"YA KAI ABDULLAHI 'DAN MUBARAK! HAKIKA ALLAH YA GIRMAMAKA (YAYI MAKA KARAMCI) KAMAR YADDA KA GIRMAMA MAHAIFIYAR MARAYUN NAN. KUMA ALLAH YA RUFA MAKA ASIRI KAMAR YADDA KA RUFA ASIRIN MARAYUN NAN".

"HAKIKA ALLAH MADAUKAKIN SARKI YA HALICCI WANI MALA'IKA NE DA SIFFARKA. YA KASANCE YANA TAFIYA TARE DA ALHAZAN GARINKU AWAJEN GUDANAR DA AYYUKAN HAJJI".

"KUMA HAKIKA ALLAH YA BAMA KOWANNE ALHAJI LADAN AIKIN HAJJI GUDA 'DAYA NE. AMMA KAI KUMA ALLAH YA RUBUTA MAKA LADAN AIKIN HAJJI GUDA SABA'IN!!".

Allahu Akbar!! Ya jama'a kunji fa!!!. Ya ku masu alfahari da yawan aikin Hajji!! (Nayi arfa sau kaza! Naje Umrah sau kaza!! Nayi dawafi sau kaza!!).

In dai yardar Allah kuke nema, ku zagaya gidajen Marayu da Miskinai da Fakirai mana! Zaku samu yardar Allah anan!! 

Ka kwashi Matanka da Qananan 'ya'yanka ka tafi dasu Umrah alhali Makwabcinka ko limamin masallacin Unguwarku, ko 'yan uwanka suna kwana da yunwa.. (Wallahi ba lallai ne Allah ya karbi Umrar taku ba). 

Wallahi ladan ciyar da Mayunwata guda goma yafi ladan zuwa Umrarka. Wasu daga cikin magabata suna cewa :



Taskar asirai malam tv AL falaki tv Ramli da hisabi tv Mafarkinka sirrinka tv Gudun duniya tv Domin Karin bayani Sai a turo SAKO ta nombarmu ko email zamu baku amsa 👇🤳 taskaasirai@gmail.com 08124763287 08144698283

Friday, 18 March 2022

SARIQUL-JINNI KASA ALJANI YA KAWO MAKA KUDI

BABBAN SIRRIN SARIQUL JINNI WANDA ZAKA SAKA ALJANI YA KAWO MAKA KUDI MASU YAWAN GASKE









Taskar asirai malam tv AL falaki tv Ramli da hisabi tv Mafarkinka sirrinka tv Gudun duniya tv Domin Karin bayani Sai a turo SAKO ta nombarmu ko email zamu baku amsa 👇🤳 taskaasirai@gmail.com 08124763287 08144698283


 

KARIN GIRMAN AZZAKARI CIKIN SAUKI

Tuesday, 15 March 2022

Logar Rubutu da Wasali da Tilawa.









Logar Rubutu da Wasali da Tilawa.
ـــــــــــــــــــــــــــــــــــــــــــــــــــــــ
Loga:- wata Hanya ce da Malaman Tsangaya suke bi don su fayyacewa Ɗalibansu yadda zasubi su Haddace Al-qur'ani da Rubuta shi cikin Sauƙi.
ـــــــــــــــــــــــــــــــــــــــــــــــــــــــ
ƴan uwa Idan ansamu kuskure a gyara, ijtihadi ne ba wahayiba dole a samu kuskure👌🏻
وهذا كله على رواية ورش👇🏻
Ita Loga anfi yin Bayaninta a wajen Darasu idan a kasamu wanda yaɓata wani Karatu, Amma duk da haka ga kaɗan daga cikin Logar Rubutu da Wasali da Tilawa.

01-Kalmar أولئك waw (و) ɗin Yana da ɗauri don haka baza'a jashi ba.

Kalmar اولىهم za'a Jaa shi saboda waw (و) ɗin ba shi da ɗauri.

Logar su idan a kasamu yamala agaban waw, Waw ɗin ba zaiyi ɗauri ba, sannan za'a Jaa shi misali اولٜىهم

Idan Kuma Babu yamala waw ɗin zaiyi ɗauri sannan ba za'a Jaa shi ba Misali أولئك haka logarsu take Babu samani.

02-Ita kuma Kalmar توعدون da Harafin ta (ت) a iya Baqara suke, Baqara da Isɗilahin Tsangaya.
توعدون......👆🏻...🌿 بقرة
03-Kalmar يوعدون da Harafin (ي) a iya Nasi suke, Nasi da Isɗilahin Tsangaya.
يوعدون......👆🏻...🌿ناس

04-Idan kaga القمر da fataha a kan Harafin Raa (ر) Shima a iya Baqara suke, Baqara da Isɗilahin Tsangaya.
القمر......👆🏻...🌿بالفتحة بقرة

05-Idan kuwa kaga القمر da Rufu'a ko kisara toh a iya Nasi suke, Nasi da Isɗilahin Tsangaya.
القمر......👆🏻...🌿بالضمة والكسرة ناس

06-Kalmar الشمس da Fataha ko Kisra a iya Baqara suke, Baqara da Isɗilahin Tsangaya.
الشمس...👆🏻...🌿بالفتحة والكسرة بقرة

07-Idan Kuma kaga الشمس da fataha ko Rufu'a, a iya Nasi suke, Nasi da Isɗilahin Tsangaya.
الشمس...👆🏻..🌿بالفتحة والضمة ناس

08-Shima wannan Karatun إن ذلك a iya Nasi ake samun su, Nasi da Isɗilahin Tsangaya.
إن ذلك ......👆🏻...🌿ناس

09-Wannan Karatun واذكر ربك shikuma a iya Baqara suke, Baqara da Isɗilahin Tsangaya.
واذكر ربك......👆🏻...🌿بقرة

10-Shima wannan Karatun واذكر اسم a iya Nasi suke, Nasi da Isɗilahin Tsangaya.
واذكر اسم......👆🏻...🌿ناس

11-Idan kaji Karatu yace خيرالكم da Fataha biyu akan Raa (ر) a iya Baqara ne, Baqara da Isɗilahin Tsangaya.
خيرالكم.....👆🏻...🌿بقرة

12-Sannan idan kaji wannan Karatun إذنادى/وإذناى/إذنادىه Duka a Nasi suke, Nasi da Isɗilahin Tsangaya.
إذ نادى......👆🏻...🌿ناس
ــــــــــــــــــــــــــــــــــــــــــــــــــــــــــــــ
                      والله أعلم 🌾

╔═════ღღ══════╗
   ✍🏻 Ibrahim Mai-sittin
         10/03/2022
╚═════ღღ══════╝
لم یتسنه🍀تلک الرسل
فبهداهم اقتده🍀انمایستجیب
هاٶماقرءواکتبیه🍀تبرک
ملق حسابیه🍀تبرک الذی
لم اوت کتبیه🍀تبرک الذی
ماحسابیه🍀تبرک الذی
عنی مالیه🍀تبرک الذی
عنی سلطنیه🍀تبرک
وماادراک ماهیه🍀سبح


(جملا بز   09)


Daga AMINU SANI ⭐ MAHUTA




Taskar asirai malam tv AL falaki tv Ramli da hisabi tv Mafarkinka sirrinka tv Gudun duniya tv Domin Karin bayani Sai a turo SAKO ta nombarmu ko email zamu baku amsa 👇🤳 taskaasirai@gmail.com 08124763287 08144698283

Kashi Na 1

MUHADARA TA MUSAMMAN KAN AZUMI 

Kashi Na 1





Abu Na Farko 'Yan Uwa Shi Addini Tsari Ne Na ALLAH Subhanahu Wata'ala Ba Malamai Ne Suka Zauna Suka Tsara Addini Ba ALLAH Ya Shar'anta Shari'a Da Kansa Ɗaya Daga Cikin Manufofi Shar'anta Addini Wa Bayi Shine Tausayi Da Jinƙan ALLAH Akan Su Bayi Soyayya Da Ƙauna 

Idan Badin Hakaba ALLAH Bashida Riba Ko Faɗuwa Wajan Shar'anta Addini

Ya Tabbata Acikin Hadisin Qudusi Al'imamu Muslim Ya Fidda Hadisin Hadisin Abu Zalrilgifari 
ALLAH Subhanahu Wata'ala Yake Cewa;

"Yaa Ku Bayina Inda Na Farkon Ku Har Zuwa Na Karshen Ku Aljanin Ku Da Mutanen Ku Duk Ku Daidaita Akan Zuciyan Mafi Tsoron ALLAH Cikin Ku Annabi Yakan Ce Nafiku Tsoron ALLAH Nafiku Bin ALLAH Sau Da Ƙafa Idan Da Kowa Bin ALLAH Sa Ɗa'a Ma ALLAH Da Bin Dokokin ALLAH Sa Kamar Manzon ALLAH Sallallahu Alaihi Wa Sallam Yake Wannan Baze Daɗeni Da Komai Ba ALLAH Yace Bazan Karu Da Komai A Iko Naba"

"Yaa Ku Bayina Inda Na Farkon Ku Har Zuwa Na Karshen Ku Aljanin Ku Da Mutanen Ku Duk Ku Daidaita Akan Zuciyan Mafi Fajircin Cikin Ku Rashin Imanin Sa Da Rashin Arzikin Sa Kamar Fir'auna Yake Ko Abu Jahalin ALLAH Yace Bazan Cutu Da Komai Ba"

In Duk Kowa Zai Lalace Kowa Zai Lalace Ace Bazebi ALLAH Ba Bazeyi Imani Ba ALLAH Yace Nifa Bazan Rabu Da Komai Ba Waɗannan Jimloli Sakon Dasuke Isar Mana Duk Wadda Kaga Ya Riƙe Addini Ya Riƙe Imani Ya Riƙe Nagarta Yafa Riƙe Ne Ma Kansa Wadda Yayi Watsi Da Addini Yayi Watsi Da Shari'a Ya Juya Baya Ma ALLAH Da Dokokin ALLAH Yayi Ne Ma Kansa Wannan Shine Ƙa'ida Na Farko Daya Kamata Ka Fahimta 

Ladan Da Yake Kiran Sallah Yana Kirane Ma Kansa Liman Da Yake Jan Sallah Yana Jan Sallah Ne Ma Kansa Inkaga Mutum Na Karanta Alqur'ani Yana Karantawa Ne Ma Kansa ALLAH Bashida Riba Ko Faɗuwa Akan Kayi Koba Kayi Ba 

🎤🎤🎤
Malam Ahmad Tijjani Yusuf Guruntum 

Muhaɗu Kashi Na Gaba 
🙏🙏🙏





Taskar asirai malam tv 08144698283

Monday, 14 March 2022

HANYOYIN DAƊEWA AKAN MACE YIN JIMAI AKAI AKAI

HANYOYIN DAƊEWA AKAN MACE

YIN JIMAI AKAI AKAI

Wato yawan yin jima'i tsakanin ma'aurata na samar da wani yanayi na juriya da daɗewa kafin su kawo (fitar mani). yawan yin jima'i kamar yawan zuwa gidan motsa jiki ne, gwargwadon motsa jininka shine gwargwadon jure wahalar sa da zaka samu. Kuma wannan zai taimaka idan ɗaya daga cikinku baya azalo (withdrawal) domin yawan yin azalo na kara maka tsahon lokaci kafin ka kawo. shiyasa ma yake da kyau ku shawarci juna ya zama ana samar da azalo koda sau daya a sati.

DAUKAR LOKACI MAI TSAHO WAJEN WASANNI

Abinda mafi yawancin mutane suka dauka shine, aiwatar da wasanni kafin saduwa baya da wani tasiri. Sabanin hakan kuwa, yin wasanni kafin saduwa yana bada gudunmawa wajen samarda yanayi na annushuwa tsakanin ma'aurata, sannan yakan kara ma lokacin kasancewa taren tsaho. misali, idan kana daukar mintuna 3 ko 4 kayi komai ka gama tare da matarka ba tare da wasanni ba, idan aka aiwatar da wasanni za'a iya samar da mintuna 8 harma zuwa 10.

FITAR DA SABBIN HIKIMOMIN SADUWA

Idan ka daɗe tare da abokiyar zaman ka, ma'ana kuka kasance na wani lokaci mai tsaho, akwai bukatar ku samar da hikimomi da zasu dinga kara ma kasancewar ku armashi. idan ya zamana kun kasance akan wani salo guda ɗaya na saduwa ko yaushe, zaku kasance cikin gundura da neman canzawa. yana da kyau ku nemi shawarwari daga masana harkar jima'i dan samun sababbin salo da zasu kara muku dadewa tare.

JINKIRIN KAWOWA (INZALI)

Idan mutuminki yana da matsalar inzali da wuri, to ga hanyar da zaki kara matsa dogon zango. lokacin da yake kanki yana sukuwa, ya kusa zuwa gaba sai ki tsayar dashi ta hanyar zare azzakarin daga farjin ki, sai bayan kamar minti biyu sai ki maida masa shi ciki. ya zamana ana samun irin haka kamar sau uku ko huɗu a duk lokacin da kuke saduwa, wannan zai sa ya zama ya kara lokaci akan yadda ya saba, dalilin wannan lattin kawowar da kika masa gwaji akai.

MURZA KARKASHIN AZZAKARIN SA

Duk lokacin da kuke tare ki dinga murza can kasan burar sa, wato kusa da golayensa. hakan yana kara masa dadewa bai kawo ba ya kuma kara ma azzakarin karfi. saidai kada kiyi kuskuren lankwasar da azzakarin a wannan yanayin domin wannan na iya jawo masa lalacewar azzakarin

KE A SAMA SHI A KASA

Wato wannan position yana taimakawa sosai wajen dadewa ba'a kawo ba. domin a haka ko wannen ku zai kasance cikin nishadi ba tare da an taɓa wurare muhimmai ba da zasu sa akawo. yadda akeyi shine, kai zaka kwanta rigingine ita kuma ta hau kanka a zaune tana dan yin gaba da baya.

MAGANI
Daga karshe, yana da kyau ku nemi shawarar masana jima'i domin baku shawarwari da kuma nuna muku irin magungunan da zakuyi amfani dasu da shawo kan matsalar ku. Ba abu ne mai kyau ba ka dinga amfani da magani kawai ba tare da sahalewar likita ba domin zai iya cutar da kai ba tare da kasani ba.

FIFIKON ANNABI AKAN AL'UMMAH (2)

FIFIKON ANNABI AKAN AL'UMMAH (2)


Salati Marashin Farko da Qarshe da tasleemi mafi cikar cika su tabbata bisa Mafi Girman dukkan bayi awajen Allah, Shugabanmu Annabinmu Muhammadu tare da iyalan gidansa Haskaka da Sahabbansa Shiryayyu da dukkan Nagartattun bayinsa har zuwa ranar da Qasa ke fidda nauye-nauyen cikinta. 

8. Yana daga cikin kebantuwar darajarsa cewa shi ka'dai ne Ummiyyi acikin Annabawa (alaihimus salam) wato ba ya karatu ko rubutu amma kuma dukkan wani mai ilimi daga hasken iliminsa ya 'dosana. 

9. Yana daga cikin kebantuwar darajarsa kasancewar acikin littafinsa (Alqur'ani) akwai ayoyin dake shafe hukuncin wasu ayoyin. Amma sauran Annabawa basu samu wannan ba. 

10. Yana daga kebantuwar darajarsa cewa shine Cikamakin dukkan Annabawa da Manzanni (alaihimus salam) Shine mafi darajarsu kuma shine Qarshen aike ﷺ

11. Yana daga kebantuwar darajarsa kasancewar Shari'arsa dawwamammiya ce har zuwa tashin Alqiyamah, Kuma addininsa ya shafe dukkan addinai da shari'o'in da suka zo kafinsa. 

12. Yana daga cikin kebantuwar darajarsa cewa an bashi ayoyin Qarshen suratul Baqarah ne daga wata taska dake Qarkashin Al'arshi. 

13. Yana daga kebantuwar darajarsa cewa shi kadai aka bama Suratul Fatiha wacce ita ce Sab'ul Mathaniy. Kuma ba'a ta'ba bama wani Annabi kafinsa ba. 

14. Yana daga kebantuwar darajarsa cewa an aikoshi ne zuwa ga dukkan mutane baki daya. Bakakensu da fararensu, da larabawa da baibayi, da kuma dukkan Aljanu baki daya. 

15. Yana daga kebantuwar darajarsa kasancewarsa shine wanda yafi dukkan Manzanni yawaicin mabiya. 

16. Yana daga kebantuwar darajarsa cewa bai ta'ba yiwa Allah laifi ba. Kuma duk da haka Allahn ya yafe masa abinda ya gabata da kuma abinda ya jinkirta. 

17. Yana daga kebantuwar darajarsa cewa shi ka'dai Allah ya bama tafkin nan na Alkauthara. Wanda ruwansa yafi Madara haske, yafi zuma zaqi, kuma yafi Qankara sanyi da da'di. 

18. Yana daga kebantuwar darajarsa cewa shi ka'dai ne Annabin da Allah ya aika zuwa ga dukkan Aljanu baki daya. Kuma yaje yayi wa'azi agaresu har ma wasu da yawa sunyi imani dashi daga cikinsu. 

19. Yana daga kebantuwar darajarsa cewa tafkinsa na Alkauthara yafi dukkan tafkunan Annabawa girma da kuma yawan masu sha. 

20. Yana daga kebantuwar darajarsa cewa Allah Madaukakin Sarki ya bashi rundunonin Mala'iku suna tayashi Yaqi a yakokinsa ﷺ

Salati da amincin Allah su tabbata bisa Annabi Muhammadu da iyalan gidansa bisa gwargwadon yawan dukkan Salatai da tasleemai da aka ta'ba yi gareshi


Sunday, 13 March 2022

MATSALAR AZZARI YA KARE QARIN TSAYI DA KAURI

AMFANONIN ZUMUNCI GA DANGI





AMFANONIN ZUMUNCI GA DANGI
منافع صلة الرحم
1. Allah yana farin ciki da mai sada zumunci.
رضا الله تعالي
2. Zumunci na haifar da farin ciki ga mai yin sa.
ادخال السرور علي المومن مع الفرح.
3. Mala'iku na farin ciki ga mai sada zumunci.
فرح الملاءكة.
4. Mai sada zumunci na samun yabo da godiya.
حسن الثناء.
5. Shaiɗan na baƙin ciki ga mai zumunci.
ادخل الغم علي ابليس.
6. Allah na ƙarawa mai sada zumunci tsawon rayuwa.
زيادة في العمر.
7. Allah na sanya albarka a cikin dukiyar mai sada zumunci.
بركة في الرزق.
8. Sada zumunci na sanya farin ciki yayin mutuwa. 
سرور لاموات.
9. Yana samun lada bayan mutuwa saboda 'yan uwa za su riƙa tunawa da shi suna masa addu'a.
زيادة الاجر بعد وفاته لان الاقربين يدعون له.
10. Sada zumunci na ƙara soyayya.
بصلة الرحم تزداد المحبة.
11. Sada zumunci na sanya ƙauna.
تقوي اواصر الالفة بين افراد الاسرة.
12. Ta hanyar sada zumunci ne dangi ke sanin junansu.
بها يتعارف افراد الاسرة.
13. Zumunci na sanya farin ciki da nishaɗi.
تدخل الفرح والسرور في قلوب.
14. Sada zumunci na sanya danƙon ƙauna tsakanin 'yan uwa.
وتقوى العلاقة الاسرية.
15. Sada zumunci na gadar da wanzuwar iyali.
صلة الرحم تحفظ النسل.
16. Sadar da zumunci na sanya mutum ya sami sakamako mai ƙyau wajen Allah.
تسير الحساب امام الله.
17. Sada zumunta na kankare zunubi.
تكفر الذنوب والخطايا.
18. Sada zumunci na zamowa dukiya cikin Aljanna.
صلة الرحم من كنز الجنة.
19. Sada zumunci na ɗaya daga cikin manyan ayyuka na gari.
هىي من أفضل الفضاءل.
Allah ya datar da mu. Ya sanya mu zama masu kusanci ga 'yan uwa da abokan arziƙi.
 Dan Allah inabukatar kayimin addu,a Allah  yasa ingama da duniya lafiya yasa intsallake kyc wassalam jabir mukhtar bello
Copying

SHIN MECECE MUTUWA? (01)





SHIN MECECE MUTUWA? (01)

Mutuwa ita ce rabuwar ruhi da jiki. Wato da zarar ruhinka ya fita daga jikinka to ka mutu kenan. Mutuwa ita ce fitarka daga wani halin zuwa ga wani.. Kuma ita ce fita daga wannan gidan (duniya) zuwa ga wani gidan (lahira). 

Allah da kansa yace Mutuwa Musibah ce.. Acikin littafinsa mai girma inda yake cewa :

"IDAN KUNA TAFIYA A DORON QASA SAI MUSIBAR MUTUWA TA SAMEKU...".

Hakika lallai mutuwa Musibah ce. Amma musibar da tafi ta girma ita ce : GAFALA (WATO RAFKANA) DAGA BARIN AMBATONTA.. Wato Mantawa da tunanin mutuwar. Da kuma rashin yin kyakkyawan tanadin guzuri saboda ranar zuwanta. 

Hakika guzuri ya kamaci mai tafiya. Shi yasa Annabinmu (sallal Laahu alaihi wa aalihi wa sallam) ya wa'azantar damu da irin wa'azin nan mai saurin tsinka zukata, Mai sanya mutum yayi ma kansa hisabi. Kuma yace : "KU YAWAITA AMBATON MAI YANKE JIN-DADI". WATO MUTUWA.

Mutuwa tana zuwa ne babu zato babu tsammani (Bagtatan). Dani mai rubutun, da ku masu karatun nan babu wanda yasan yaushe zai, mutu ? A wanne waje zai, mutu? Da yaya zai mutu? Kuma menene ajalinsa?. 

Wannan ita ce babbar tambayar da bata da amsa.. Kuma babu wani daga cikin mutane wanda ya santa balle ya gaya maka.. Shima bai san tasa ba, balle yasan ta wani. 

Allah yana cewa : "ALLAH AWAJENSA NE SANIN ALQIYAMAH YAKE, KUMA SHI KE SAUKAR DA GIZA-GIZAI KUMA YASAN ABINDA KE CIKIN MAHAIFA. 

"BABU WATA RAI WACCE TASAN ABINDA ZATA TSUWURWURTA GOBE, KUMA BABU WATA RAI DA TASAN AWACCE QASA NE ZATA MUTU".

Hakika mantuwa ko rafkanuwa daga tunanin Mutuwa da 'dacin nan nata, da Kwanciyar Qabari da duhun nan nasa, Da tambayoyin nan na Mala'iku da tsananinta, da ranar Alqiyamah da Tashin hankalin nan nata, da hawan siradi da kaifin nan nasa, Mantuwa daga ambato ko tunanin wadannan yakan sanya zuciya ta bushe har ma alfasha da 'barna su bayyana acikin doron Qasa da teku.. 

Ka sani cewar idan kai mai tuna mutuwa ne, to zaka kasance mai tanadin guzuri domin zuwanta..

Shin yaya sallarka take? Shin kana yinta akan lokacinta, tare da Ikhlasi da tsoron Allah? Shin kana da ilimin sanin tsarki da alwala da hukunce-hukuncen Salla?. In baka dashi mai ya hanaka ka nema?? -- Neman duniya ko? 

Yaya azuminka yake? Shin kana tsaftace idanunka da harshenka ayayin da kake azumi? Shin kana kiyayesu daga kallon haramun, ko furta kalmomon haramun? Ko tunanin aikata sa'bon Allah??.

Shin yaya bin iyayenka yake? Shin kana basu hakkinsu kamar yadda ya dace? Baka 'bata musu rai, baka yi musu tairin kai da girman kai? Shin baka fifita matarka ko abokanka akansu?. 

Yaya sadar da zumuncinka yake? Shin kana hakuri da wautar 'yan uwanka? Shin kana basu hakkinsu? Kana kyautata musu? Kana ziyartarsu?. Ko ko ka biye ma zuciya kana rama mugunta da mugunta?. 

Yaya Mu'amalarka da mutane take? Shin kana sakin fuska ga dukkan Musulmai? Shin kana girmama kowa, kana zaman lafiya da kowa? Shin kana kwatanta adalci da gaskiya da rikon amana acikin kowacce harka ta cikin gidanka da wajen aikinka ko kasuwarka?.

Yaya dukiyarka take? Yaya abincinka da abin shanka yake? Ka tabbatar kan cin halal dinka kana kiyayewa daga haram?. 

Idan akwai matsala yi kokari ka gyara.. Domin mutuwa tana daf da kai.. Mala'ikan mutuwa kullum yana shafa kanka sau saba'in.. Zai iya chafke ruhinka duk sanda aka umurceshi.. 

NASIHA CE DAGA ZAUREN FIQHU



KHAMSUNA HADISI• •HADISI NA 19•

Manzon ALLAH {s.a.w} Yace: Kada kuci da hannun hagu, domin shaiɗan ne keci da hannun hagu.

[Ibn majah]

DARASI:

Ma'ana haramun ne cin wani abinci da hannun hagu.

kuma cin abinci ko sha da hagu yana iya jawowa mutum karɓar sakamakonsa da hagu a ranar Alƙiyama.

Ba ɗabi'ar mumini bace cin abu da hannun hagu.

•HADISI NA 20•

Manzon ALLAH {s.a.w} Yace: Kada ɗayanku yasha abinsha a tsaye.

[Muslim].

DARASI:

Haramun ne shan abinsha a tsaye ko cin wani abu a tsaye.

Saidai mutum ya zauna ko a tsuguna.

Duk wanda yake shan abun sha a tsaye to baya daga cikin mabiya umarnin ALLAH da Manzonsa {s.a.w}.

Ansamu a hadisi cewa Manzon ALLAH {s.a.w} ya sha abin-sha a tsaye, amma idan aka duba waɗannan hadisai sosai za'asamu akwai dalili dayasa ya aikata hakan.

Saboda kiyayewa shine abu mafi alkhairi.

•HADISI NA 21•

Manzon ALLAH {s.a.w} Yace: Kada ɗayanku yayi tafiya da takalmi kafa ɗaya.

[Bukhari da Muslim]

DARASI:

Haramun ne mutum yayi tafiya da takalmi guda ɗaya, sai dai ko ya cire dukka ko kuma ya saka dukka.

Saboda idan takalmin ɗayanku ya tsinke to ya cire dukka kada yayi tafiya acikin takalmi guda ɗaya.

Duk mai aikata haka zai sami kansa acikin fushin ALLAH, kuma sami kansa cikin mummunan hali saboda rashin bin Umarnin ALLAH da manzonsa {s.a.w}.

ALLAH shine mafi sani.

ALLAH kabamu ikon aiki da abinda muka karanta.

ALLAH ka gafarta mana zunubanmu baki ɗaya.
Ameen...


Friday, 11 March 2022

KARATUN TAFIN HANNU 1 AND 14




ASSALAMUALAIKUM YAN UWA ALMAJIRAI MASOYA ANNABI MUHAMMADU S A W MUNA MUKU BARKA DA WANNAN LOKACI YAU  ZAMU CIGABA DA KARATUN TAFIN HANNU 👇🤳🏦 


 

SAHABBAI GOMA DA AKA YIWA BUSHARA DA ALJANNAH




SAHABBAI GOMA DA AKA YIWA BUSHARA DA ALJANNAH 

👉 1. Abubakar Assiddik.
👉 2. Umar Dan Khaddab.
👉 3. Usman Dan Affan.
👉 4. Aliyu Dan Abi Dalib.
👉 5. Dalha Dan Abaidullahi.
👉 6. Zubairu Dan Awwam.
👉 7. Abu Ubaida Dan Jarrah.
👉 8. Abdurrahman Dan Aufu.
👉 9. Sa'adu Dan Abi Wakkas.
👉 10. Sa'idu Dan Zaid.

SHIKA SHIKAN MUSULUNCI GUDA BIYAR 

👉 1. Tauhidi.
👉 2. Sallah.
👉 3. Azumi.
👉 4. Zakkah.
👉 5. Hajji.

SUNAYEN WATANNIN MUSULUNCI : 

👉 1. Almuharram.
👉 2. Safar.
👉 3. Rabi'ul Awwal.
👉 4. Rabi'ul Sani.
👉 5. Jumadal Ula.
👉 6. Jumadal Akhirah.
👉 7. Rajab.
👉 8. Sha'aban.
👉 9. Ramadhan.
👉 10. Shawwal.
👉 11. Zulkidah.
👉 12. Zulhijji.

Ya Allah duk wanda ya taimaka wajen yada wanan ilmin don wasu su amfana; 
Ya Allah ka haskaka rayuwarsa da annurinka, 
Kasa yayi kyakkyawar karshe,
Ka sashi a inuwar Al'arshenka ranar  Alkiyama,
Kuma ka shayar da shi ruwan Alkausara,
Ya Allah ka sa mu  ziyarci juna a gidan Aljannah,
Amin Summa Amin 👏🏻👏👏👏👏👏👏👏

RANAR ALKIYAMA TSAYAWA GABAN ALLAH




Ranar Al Qiyama Kowane Mutum Idan yatashi Abinda yake Qira: Nafsi Nafsi, Annabawa Da Manzanni= Nafsi Nafsi, Iyaye Da Yara= Nafsi Nafsi, Mata Da Maza= Nafsi Nafsi A ranar Shugaba Dayane Shine Annabi Muhammad Rasulullahi {S.a.w} Farkon Tashi Zaice Aina Ummati Aina Ummati Allahu Akabar 'Yan Uwa Kutuna fah yana Da Dangi Amma Daya Tashi Baice Ina Dangi Naba Sai Yace Ina Al'ummata, 'Yan Uwa ko Dan Wannan Bama So Annabi Ba 'Yan Uwa Dan Qaunar Ka/Ki Da Annabi Ka Tura Wannan Zuwa Grp 3 Ko Mutane 3 Ya Allah Ka Samu A Cetan Annabi Muhammadu {S.a.w}. Allah kasa mudace
ALBAKACIN ANNABI S,A,W,   ka tsaya KAKARANTA 
Ya allah ka kare duk wani musulmi daga sharrin.🙏

•Zina
•Luwadi
•Madigo
•Istimina'i
•Sata
•Zalunci
•Munafurci
•Qunchi
•Bashi
•Hasda
•Keta
•Zulama
•Talauchin Duniya da Lahira.

Don alfarmar fiyeyyen halitta Annabi (S,A,W) kadaure kayi share zuwa groups (5)🙏
🔗
🔗 

Ya Allah Ka Karawa Duk wani Musulmin Duniya.

•Lafiya
•Hakuri
•Juriya
•Lafiya
•Karfin imani
•Hankali da Tunani mai kyau
•Mace tagari
•Minji na Gari
•'Ya'ya Na Gari
•Abokan Zama na Kirki
•Arzuki Mai Amfani
•Wadatar Zuci
•Ya Allah Karufawa Duk Wanda Ya
Karanta Wannan Sako Yayi share a groups Yace Ameen
Asiri Duniya da Lahira.

don Allah ☝️ kadaure kayi share zuwa groups 5 👌

SIRRIN BARHATIHIN NA ISMUL AZIM MAI GIRMA




SIRRIN BARHATIHIN NA ISMUL AZIM KADA KA BAWA WANI WANNAN SIRRIN SAI DANKA WANDA YAYI MAKA HIDIMA  SIRRI NE DA AKE BOYE SHI SABODA GIRMAN SHI


 



 

MAULANA SHEHU IBRAHIM NIASSE(R.A) Yana Cewa:-

MAULANA SHEHU IBRAHIM NIASSE(R.A) Yana Cewa:- "Bushewar Zuciya, Itace Mafi Girma a Cikin Bala'i Bayan Kafirci. Akwai Ayyuka Guda 24 Dake Busar Da Zuciya, Wanda SHARI'A Bata Yarda Da Su Ba, 'DARIKA Bata Yarda Dasu Ba, Hakama HAQIQA Bata Yarda Dasu Ba Sune Kamar Haka:- 1 - Mutum Ya Tsaya Akan Zunubi Guda Daya, Yayi Tayi Yana Maimaitawa. 2 - Tsawon Buri, Mutum Ya Zama Bai Wadata Da Abinda ALLAH Ya Bashi Ba. 3 - Yawan Fushi, Ba Akan Tafarkin ALLAH Ba. 4 - Musulmi Ya Riqe Dan'uwansa Musulmi a Zuciya. 5 - Son Duniya Kota Halin Yaya. 6 - Son Girma, Cikin Kowane Hali. 7 - Katsalandan a Harkar Da Ba Ruwanka a Ciki. 8 - Yawan Dariya, Mutum Ya Zama Kamar Wawa. 9 - Yawan Zolayar Mutane. 10 - Jindadi Saboda Abin Duniya, Har Kamanta Da ALLAH Saboda Farin Ciki. 11 - Baqin Ciki, Yayin Da Jindadi Ya Zo Ya Koma. 12 - Gafala Ga Barin Zikirin ALLAH. 13 - Rafkana Ga Barin Tunanin Lahira. 14 - Barin Yin Tunani Akan Sha'anin Wuta. 15 - Barin Yin Tunani Akan Sha'anin Aljannah. 16 - Yawan Yin Firar Banza. 17 - Yawan Yin Abota Da Wawaye. 18 - Da Yawan Cin Haram. 19 - Mugun Cin Abinci. 20 - Da Yawan Janyo Sha'awa. 21 - Yawan Barci 22 - Yawan Tunanin Banza 23 - Qarancin Ambaton ALLAH 24 - Jiji Da Kai KAJI BABBAN LIKITAN ZUCIYA MUN GODE SHEHU! ALLAH YA TSARE MANA ZUCIYOYINMU DAGA BUSHEWA AMEEEN.

Wednesday, 9 March 2022

MUWATTAH IMAM MALIK• •HADISI NA 36•



•MUWATTAH IMAM MALIK• 

•HADISI NA 36• 

Yahya ya bada Labari Daga Imam Malik (Rh) daga Yahya Ɗan Muhammad Ɗan Ɗahla'a daga Usman Ɗan Abdurrahaman cewa:

Babansa ya zantar dashi cewa: Shi yaji Sayyadi Umar Ɗan Khattab (RA) Yana yin Alwala fiyeda abinda yake ƙasan mayafinsa.

DARASI:

Wannan hadis yana mana nuni da halaccin yalwatawa acikin Alwala, wato mai Alwala zai iya wanke sama da gwiwar hannunsa koda yakai kusa da kafadarsa babu komai.

hakama ƙafarsa yana iya wankewa har izuwa ƙaurinsa.

• Yahya Yace: An Tambayi Imam Malik (Rh) Gameda wani mutum da yayi Alwala sai ya mance ya wanke fuska a maimakon ya fara da kurkure baki.

Ko kuma ya wanke hannayensa zuwa wuyan hannu wato zira'i kafin ya wanke fuskarsa, sai yace:

Yana mai amsa wananna tambaya:

Wanda ya wanke fuskarsa kafin kurkurar  baki, to ya kurkure bakin kawai ba sai ya sake wanke fuskarba.

Wanda kuma ya wanke hannunsa izuwa wuyan hannu kafin ya wanke fuskarsa, to ya wanke fuskarsa, sannan kuma ya sake wanke hannayensa zuwa wuyansu har sai ya wankesu bayan wanke fuska.

Idan ya kasance yana nan agun da yayi Alwala, ko kuma hakan ya farue a wajensa.

•Yahya Yace: Antambayi Imam Malik (Rh) Gameda mutumin da ya manta da kurkurar baki kuma ya manta da shaƙar ruwa a hancinsa bai tunaba har sai da yayi salla, sai yace:

Ba zai sake wata sallarba, kawai zai kurkure bakinsa ne, kuma ya shaƙi ruwa daga baya, Idan yana son yin sallah da wannan Alwalar.

ALLAH shine mafi sani.

ALLAH ka bamu ikon aiki da abinda muka karanta.

ALLAH ka gafarta mana zunubanmau baki ɗaya.
Ameen...

MATSALAR AZZARI YA KARE

Tuesday, 8 March 2022

TARIHIN RAYUWAR MA,AIKI S,A,W (1)

 Da Sunan Allah Mai rahama Mai Jin}ai, godiya ta tabbata ga Allah 
Ubangijin halittu, tsira da amincin Allah su tabbata ga Annabi Muhammad (SAW) da iyalansa da zuriyarsa da sahabbansa da wa]anda suka biye musu
game da wa]an nan ~angarori, ina ro}on Allah Ya gafarta mana
Faru}i ya fassarasa da harshen Turanci daga harshen Turancia ]ab’i na 
duk in da na ga haka, na kan ce: ban san in da mai littafi ya ciro wannan 
(mustashiri}ai) suka samar na }arya dangane da rayuwar Muhammad 
kawo fassarar wasu ayoyi da wasu hadisai wa]anda ba su inganta ba, wanda 
fassara da harshen Turanci bai cika kawo in da ya ciro labari ba, don haka 
kuma mayalwaci kamar wannan wadda ta ]auki nauyi wajen fassara shi 
babu wani littafi na tarihin Manzon Allah(SAW) wanda ya ke da girma 
na yi iya }o}ari na wajen gyarawa tare da kawo hadisai da suka inganta 
da kyawon aiki har zuwa ranar sakamako.
Hajiya Daula Justice Muhammad Bello, ta yi tunanin wannan aiki ne, saboda 
ba, amma na bayyana wasu daga cikinsu a ta}aice, kuma mai littafin ko mai 
wan nan aiki Ya sanya Aljanna ce makomarmu. 
takwas. Saboda haka Hajiya Daula Justice Muhammad Bello ta ]auki nauyin 
Is’ha} Yunus Muhammad Tukur Almashgool Bauchi na fassara daga 
kuskurenmu. Wannan littafi ya yalwata magana akan wasu ~angarori na 
Muhammad Husain Haikal ya wallafa, kuma Sheikh Isma’il Raji A. Al
zuwa harshen Hausa. Kuma shi mai littafin da wanda ya yi wa littafin 
~angarori da suka shafi tarihi. Musamman tarihin da Orientalists 
fassara sun sami kansu wajen bin ra’ayin Orientalists musamman wajen 
tarihi amma bai cika kawo labarin da aka sani cikin }ananun litattafan tarihi 
(SAW) da abubuwa da suka shafi addininMusulunci, Allah Ya kar~a mana 
 Bayan haka ina fatar jama’ar Musulmai za su amfana da wannan littafi mai 
muhimmanci Allah Ya saka mata da alherinSa. Kuma ina mi}a godiya ta ga 
 Wannan tarihi na wani littafi ne, wanda aka yi masa fassara zuwa harshen 
ba, saboda haka mai karatu zai ga wasu ya}e-ya}e da Annabi (SAW) ya 
aiwatar, bai ambace su ba. Haka kuma siffofin Annabi (SAW) bai ambace su 
labari ba. Kuma na kanyi }o}arin kawo abin da ya tabbata gwargwadon iko, 
saboda wannan fassara na yi shi ne cikin kwanaki arba’in daidai. 
Muhammad Bello wadda ta ]auki nauyin fassarar wannan littafi, mai 
Hausa, mai suna kamar haka: ‚The Life of Muhammad (SAW),‛ wanda Dr. 
 Daga }arshe ina mi}a godiya ta musamman ga Hajiya Daula Justice 
muhimmanci, musamman masu magana da harshen Hausa. Saboda haka 
fassara, kamar yadda mai karatu zai fahimci mafarin wannan fassara. Ni 
harshen Turanci zuwa harshen Hausa, ta re da yin wasu gyare-gyare a wasu 
mata ta Malama Suwaiba Sa’id Muhammad Awwal saboda gudummuwar da 


Monday, 7 March 2022

Hijabi lulluɓin musulunci 🧕 _Gudummawar da musulunci ya bayar akan mace

🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦

⚜️⚜️⚜️Daga⚜️⚜️⚜️
🧕 Hijabi lulluɓin musulunci 🧕

_Gudummawar da musulunci ya bayar akan mace

📝 Ibraheem y. Ibraheem

Bismillahi rahmanirrahim
______
Haƙiƙa Musulunci ya haifar da gagarumin sauyi a tarihin mace‚ wanda har ya zuwa yau ba a samu na biyunsa ba. Domin ta hanyar sa ne‚ ta samu damar dawo da mutunci da haƙƙoƙinta da aka raba ta da su  a ƙarƙashin zaluncin zamanin jahiliyyah na ƙarnoni da dama.Ta hakane musulunci ya ƙwato mata haƙoƙin ta yadda zata yi rayuwa cikin aminci da mutunci ƙarƙashin tsarin rayuwa mafificiya.

A karo na farko a tarihi‚ Mace ta samu damar amfana da haƙƙoƙinta na ɗan'adamtaka a ƙarƙashin tsari da dokoki irin na musulunci. An yaye wa mata‚ ƙangin zalunci‚ kana kuma at samu damar rayuwa a matsayin ɗan Adam mai mutunci‚ ɗaukaka kana mai matsayi kamar dai-dai da na miji. To amma fa dole ne wannan  ’yanci ya kasance cikin iyakokin Allah.

Maɗaukakin sarki Wanda ya bawa Mace dama‚ kana kuma ya tsara Mata hanyar da za ta iya ba ba nata gudunmawar wajen gina ɗaukaka‚ ta tabbatar da gaskiya da kuma yaɗa alheri.

Yaɗa alheri ɗin kuwa shine ta kiyaye mutuncin ta wajen sanya yalwataccen sutura‚ da sanya kammalallen Hijabi‚ yanda musulunci ya ta nadar.... Mafarki da tatsuniya ba wajen waɗansu‚ idan har ba a ƙarfafa shi da ayoyi na Alqur'ani mai girma da hadisan Annabi da kuma mutanen gidansa {Ahlulbait} tsira da amincin Allah su ƙara tabbata a gare su.

1_ A zamanin jahiliyyah‚ al’umma tana ganin mace wata bi-tsami‚ Wani abu na la’alana‚ ma tatta-irin muggan ayyukan shaiɗan‚ ko kuma sukan kwatanta ta da matsayin Wata dabba ala halicce ta a yanayin ɗan adam. To amma ko da Alqur'ani yazo sai ya ƙaryata wannan ƙuduri‚ wanda saɓa wa gaskiya da kuma haƙiƙa.


Yaƙe yar uwa “sister” keda musulunci ya baki wannan gagarumin guduma wa miye naki bayyana tsaraicin ci ta hanyar amfani da sa gyale‚ ko tufafin da zai bayyana surar jikin ki‚ bayan kina aikata laifi ne mafi girma. Wato zunibi‚  yaci gaba da cewa namiji da mace irin ’yan tagwaye ne da suka fito daga maɓuɓɓuga da kuma manufa Guda.


“....ya ku mutane ! Ku bi Ubangijinku da taƙawa‚ wanda ya halicceku Daga Rai guda‚ kuma ya ya halitta‚ daga gareshi‚ ma’au-ransa‚ Kuma ya watsa gada gare su maza masu yawa da mata....”

Bayan bayyana matsayin mace a Rayuwa da kuma samuwar ɗan’adam a fili‚ Alqur'ani mai girma ya yi kakkausar suka Ga al’adar nan ta bisne ’ya’ya Mata da rai‚ wato wa’id {4}.....“kuma idan wanda aka turbuɗe ta da rai aka tambaye ta‚ Saboda wani laifi ne aka kashe ta”?5Kana kuma kuma ya kawo karshen zamanin da ake kange mace daga Aure har sai biya kuɗin fansar kanta ko kuma cikin zalunci a gaje ta bayan mutuwarta.


“....Ya ku waɗanda suka yi! Imani ba ya halatta a gare ku‚ ku gaji Mata a kan tilas. Kuma Kada ku hana su Aure domin ku tafi da shashen abin da kuka basu.....”6
Sannan kuma ya yaye musu irin zalunci da wulaƙanta su da mazaje suke yi. Don haka ne ma Alqur'ani ya ba da muhimmanci mai girman gaske akan tausaya musu yayin mu’amala da su:

“.... kuma kuyi zamantakewa da su da alheri. Sa’an nan idan kun ƙi su‚ to‚ akwai tsammanin ku ƙi wani abu‚ Alhali kuwa Allah ya sanya wani alheri mai yawa a cikinsa.....”7
Ko da yake a da‚ talauci ma ya kan sa mutane su kashe ’ya’yansu musamman ma ’ya’yaye mata‚ Don haka Alqur'ani ya kawar da wannan al’amarin {daga kanta}:

In Sha Allah zamu dakata anan sai in Allah ta'ala ya kaimu sati na Gaba zamuci Gaba in Sha Allah. Abin da muka faɗa da-,dai Allah ya bamu ladansa, kurakurai Allah ya ya yafe mana. Ma assalawat ala Muhammad wa Ali Muhammad 🌹

اللهم على محمد وال محمد وعجل فرجهم وانصرجيوش المسلمين، سبحان ربك رب العزة عما يصفون وسلام على المرسلين والحمد لله رب العالمين، الفاتح


_WASIKA✍️ ZUWA GA MATASA👳🏻‍♀️ MASU AIKATA ISTIMNA'I🤏_*

*_WASIKA✍️ ZUWA GA MATASA👳🏻‍♀️ MASU AIKATA ISTIMNA'I🤏_*

*ma'anar ISTIMNA'I shine= fitar da mani ko sha'awa da gangan ta hanyar da bata dace ba.*

Matasa Maza da mata, suna neman taimako akan illolin da suke samu a jikunansu sakamakon Istimna'i wato Masturbation. An kawo hujjoji
gamsassu daga Al-Qur'ani da Sunnar Ma'aikin Allah (saw) da fatawoyin Amintattun Malamai duk akan HARAMCIN ISTIMNA'I, Amma duk da haka wasu matasan basu yarda sun dena ba. 

Wasu kuwa sunji tsoron ALLAH sun riga sun dena, bubban dalilin da yake janyo musu afkawa cikin
wannan bala'in shine :

1. Kallon Fina-finan batsa.

2. Shiga shafukan internet na batsa.

3. Yin zantukan batsa tsakanin
saurayi da budurwa.

4. Kusantar zina ta hanyar kallo da
shafa, ko zance da dai sauransu.

Wasu kuma suna aikata hakan ne
dan gudun afkawa ZINA, basu san cewa shi d'inma ZINAR bane!!

Idan kun Qi bari domin Allah, to ku dubi irin illolin da yake haifar muku ajikinku mana!!!

1. MUTUWAR IDANU.

2. MUTUWAR AL'AURA.

3. CIWON BAYA.

4. BUGAWAR QIRJI.

5. RIKICEWAR TUNANI.

6. YAWAN MANTUWA.

7. KARANCIN 'YA'YAN MANIYYI.

8. SAURIN INZALI.

9. SHAFAR ALJANU, ETC.

Wad'annan 'yan kad'an ne daga cikin Matsalolin da ISTIMNA'I yake haifarwa. kuma duk wanda bai tuba ya dena ba, idan ya mutu a haka zai je ya tarar da hisabi.

DAN GIRMAN ALLAH!! Matasa ku kiyayi zina da duk dangoginta, ku Qaurace ma duk wani abinda zai rinQa motsa muku sha'awa, idan
da hali kuje kuyi aure, idan kuma babu hali, to ku yawaita azumi.
ALLAH YA SAUWAQE

Don Allah 'Yan uwa MAZA DA MATA,
DON ku taya mu isar da wannan sakon ta hanyar Sharing a FACEBOOK, TWITTER, BBM WHATSAPP, da sauransu. Insha Allahu wasu da yawa zasu amfana.
Manzon Allah (s.a.w) yace: "WALLAHI IDAN ALLAH YA SHIRYAR DA MUTUM GUDA TA
DALILINKA, YAFI ALKHAIRI GAREKA FIYE DA ABAKA JAJAYEN RAQUMMA"
*Wani mutum yazo wajen manzon Allah S. A.W. ya ce: Yah-Manzon-rahma zan tambaye ka rayuwar duniya da ta lahira.*

*1.  Yah Manzon Allah ina son in zama mafi sani a cikin mutane?*
*AMSA* 
*Sai ya ce "Ka ji tsoron Allah ka bi dokokin Sa."*

*2.  Ina son in zama mafi arziQi a cikin mutane?*

*AMSA*

 *sai ya ce "Ka zama mai wadatar zuci."*

*3.  Ina son na zama Wanda yafi kowa acikin mutane?*

*AMSA*

*Sai ya ce "Ka zama mai amfanarwa."*

*4.  Menene zai kare ni daga wuta?*

*AMSA*

*Sai ya ce "Ka zama mai yawan yin Azumi."*

*5.  Ina so in zama mafi adalci a cikin mutane?*

*AMSA*

*Sai ya ce "Ka so ma d'an uwanka abin da ka ke soma kanka."*

*6.  Ina son in zama mafi amfanin mutane a wajen Allah?*

*AMSA*

*Sai ya ce "Ka yawaita tuna Allah."*

*7. Ina son imanina ya zama ingantacce?*

*AMSA.*

*Sai ya ce "Ka gyara halayen ka."*

*8.  Menene yake huce fushin Allah  (S.W.T.)?*

*AMSA*

*Sai ya ce "Ba da zakka a boye da kyautata ma 'yan uwa."*

*9. Wani zunubi yafi muni awajen Allah?*

*AMSA*

*Sai ya ce "Mummunar hali shine rowa"*

*10.  Ina so in zama mafi biyayya ga Allah?*

*AMSA*

*Sai ya ce "Ka bi umurnin Allah za ka zama mafi rinjaye a wurin Allah."*

*YA ALLAH Ka sa mu gama da Duniya lafiya.*

*INA ROQON MAI KARATU dan GIRMAN ALLAH DAN SON ANNABI kayi Qokari ka tura wani group d'in domin tunasarwa....🙏🏻🙏🏻🙏🏻 Mungode*
             



            

QALUBALE GA DUKKAN BATIJJANE !!!*

*QALUBALE GA DUKKAN BATIJJANE !!!*

*⌛DABARAR YAN SHI'AH NA SHIGOWA CIKIN TIJJANAWA, DA YAUDARARSU DA KARBAR DARIQAR TIJJANIYYA DON SUYI AMFANI DASU WAJEN CUSAWA MASU KARANCIN ILIMINSU AQIDAR SHI'AH BA TARE DA SUN SANI BA⌛*

*KASHI NA FARKO:*

*MAUDHU'I: MENENE YASA YAN SHI'AH SUKA ZABI SHIGA CIKIN TIJJANAWA AKAN SAURAN DARIQU DA AQIDUN DA MUKE DASU A AFRICA ?*


*Muna fara wannan rubutu da sunan mamallakin halitta baki daya. Wanda ya samar da samuwa don a bisa zabinsa, ya kuma saukar da tsarin da yake so halittunsa su kasance akansa. Tsira da amincin allah su kara tabbata ga shugaban samammu, wanda allah ya samar da halitta saboda bayyanar da girmanshi da isarsa a wajenshi, wato annabi muhammadu (s.a.w). Allah kasa da ahalinsa madaukaka, da sahabbansa masu girma, da duk wadanda suka biyo bayansu da kyautata ayyuka cike da tsarkin zuciya har izuwa ranar karshe.*


*GABATARWA:*

*Hakika munyi zurfin tunani, da nazari, hade da duba da bincike akan abinda yake nema ya rikita tsarin tafiyar Yan darikar tijjaniyyah a wannan lokaci da muke ciki, ta yanda muka ga yadda Samarin darikar tijjaniyyah da yawa suna sauka daga tarbiyyar dariqar tijjaniyyah izuwa aqidun shi'ah ba tare da sun sani ba, harma suna daukar hakan a matsayin burgewa da cinyewa a cikin tafiyar darikar tijjaniyyah. Hakan yasa samarin da suke cikin wannan matsala firgicewa da sambatu na maganganun da basu da tushe bare makama a cikin darikar tijjaniyyah.*


*MAUDHU'I: MENENE YASA YAN SHI'AH SUKA ZABI SHIGA CIKIN TIJJANAWA AKAN SAURAN DARIQU DA QUNGOYOYIN ADDININ MUSULUNCI DAKE AFRICA ?*

*Hakika duk wanda ya san qididdiga da kiyasin mutanen africa musulmai dole zai san babu musulman da suka fi yawa kamar yan darikar tijjaniyyah. Sannan babu mutane masu saurin yarda da wankakkiyar zuciya kamar tijjanawa. Duk wanda yace yana son annabi (s.a.w) zasu soshi, kuma zasu iya yi masa komai yake so matukar basu ga sabawa umarnin allah akan hakan ba. Sannan basu da mummunan zato ga duk wanda ya bayyana musu kyakykyawan abu. Abinda ka bayyana musu shi zasu dauka musamman idan abun mai kyau ne, ba zasu biyo bayanka da zargi ko tuhuma akan abinda ka bayyana musu na kyakykyawan furuci ko aiki.*

*Wadannan abubuwa sune suka zamo lagonsu da duk mai son cutar dasu ko yaudararsu yake amfani dasu matukar ya sansu. Sun san da wannan, kuma sun san ana amfani da hakan wajen cutar dasu amma basu canja ba daga wannan kyakykyawar zuciya tasu.*


*MAFARIN ZANCE:*

*Hakika Yan shi'ah mutane ne masu fadada bincike da iya tsari, da kuma yin dogon shiri don cimma muradinsu. Suna iya rikidewa izuwa kowace siffa, sannan suna iya daukar tsawon lokaci suna shirya shirinsu na makirci akan wanda suke so suyi nasara akansa. Sannan suna da kokarin yin karatu don ya zamo musu makami wajen samun nasarar shawo kan mai mai karamin sani dangane da lamuran addini.*

*Hakika sunyi nazari akan tijjanawa sosai. Kuma duk awonsu yayi daidai da bukatarsu.*

*Basu da karfin jama'ah na zahiri da kuma yardar mutanen gari, da zasu iya yin amfani dasu wajen yada da'awarsu ta shi'ah. saboda haka; Suna son su samu karfin jama'ah, sannan kuma su samu wadanda zasu yarda dasu ba zasu koresu daga garesu ba, sannan wadanda zasu amince su mu'amalancesu da zuciya daya ba tare da zargin akwai wata manufa a karkashin zuciyarsu ba da suke son isarwa. saboda haka sai suka duba suka ga wadanne musulmai ne masu yawan da zasu iya rabuwa dasu don su samu karfi daga karfinsu, sannan su shigar da akidunsu cikinsu ba tare da sun sani ba ?*

*Sai suka ga tijjanawa ne suka fi kowa yawa a africa, Hakane yasa suka zabi shigowa cikin dariqar tijjaniyyah don tijjanawa su yarda dasu, su dauka tare suke dasu. Don su saki jiki dasu. Sannan idan wani zai kawo musu hari tijjanawa su zama garkuwarsu. Sannan su samu damar shiga guraren da a baya basu isa su shigesu ba saboda ba'a yarda da akidarsu a wajen ba. Amma ra'buwarsu da darikar tijjaniyyah sai ya zama sun shiga wajen da lasisin darikar tijjaniyyah. Ta hakan sai suyi da'awar tijjaniyyah kunshe da manufar isar da akidojin shi'ah ga mutanen da basu san kansu ba.*

*Wannan shine dalilin da yasa Yan mazhabar shi'ah suka zabi shiga darikar tijjaniyyah akan sauran dariku da qungiyoyin addini da suke africa.*



*ZAMU DORA A RUBUTUNMU KASHI NA BIYU INSHA ALLAH.*

*INDA ZAMU JI MENENE YAN SHI'AH SUKA FARA YI KAFIN SU FARA ISAR DA MANUFARSU A CIKIN TIJJANAWA, DON NEMAN YARDAR TIJJANAWA, BAYAN SUN SHIGO DARIQAR TIJJANIYYAH ?*

*RUBUTUNMU KASHI NA BIYU ZAI ZO ANAN KUSA INSHA ALLAH.*

Domin samun mustajaba a kwana 9

 Khatimin Allahu Muhammadu  idan ka buga adadin Allahu sau Allahu 66×66=4356 sannan sunan Muhammadu sau  92×92=8464 4356+8468=12820 Ana rubu...