Tuesday, 26 April 2022
Thursday, 21 April 2022
Tuesday, 19 April 2022
Monday, 18 April 2022
Sunday, 17 April 2022
ASÃRA MAFI GIRMA AWA
ASÃRA MAFI GIRMA AWATAN RAMADÃN
══════ ❁✿❁ ═══════
TA FARKO.
Kai Baka Tsaya Anyi Sallar-Tarãwĩhi da Kai ba, Kuma Kai Baka Tãshi Cikin Dare Kãyi Wata Ibdah ba, Sa'annan daga Cin Abincin Sahur, Ka Koma Bacci Baka Sãmu Sallar-Asubahi ba.
LALLAI KA TAFKA ASÃRA
══════ ❁✿❁ ═══════
TA BIYU.
Ramadãn Na Neman Tafiya, Amma Har Yanzu Baka Sauke (ALQUR'ÃNI) Koda Sau ɗaya ba, Gãshi Kai Bãbu Ruwanka da Zuwu Jin Tafsĩri, Kã Kãsa Zuwa Kõda Na Yini ɗaya, Kuma 'Yar Sadakar Nan da Ake Kaiwa Masallaci Don Taimakon Marãyu, Ko Dabĩno da Ruwan Sanyi da Ake Kaiwa Don Sãmun Lãdan Masu Azumi, Babu Kai Aciki.
WANNAN BA 'KARAMAR ASÃRA BANE
══════ ❁✿❁ ═══════
TA UKU.
Ana Azumi Amma Kai Babu Ruwanka da Ambaton Allah, Sai Buga Game a Handset da Kallace-Kallencen Finãfinai da Gulmace-gulmace, da Musun-banza, Kuma alla-alla Kake yi Asha Ruwa Ka Kēta Alfarmar Daren Ramadãn da Sãbon Allah.
HM, ANYA KUWA!!!?
══════ ❁✿❁ ═══════
TA HU'DU.
Asãra Mafi Girma da Zaka Tafka Shi Ne: A Sãmu Daren (Lailatul-Qadr) Yazo Ya Wuce Kana Shirga Bacci, Ko Kana (Night-Browsing) Wanda Meyuwu wa, Wannnan Azumin Shĩne: Na 'Karshe A Rãyuwar ka Baka Sani ba.
ALLAH YA KYAUTA
══════ ❁✿❁ ═══════
#NASIHA
Kana da Sauran Lokacin da Zaka Rĩbata, Kwana (14) Ko (15) Suka Rage Maka, Wanda Acikin Su Ne (Lailatul-Qadr) Yake, Kada Kace Sai A Goman 'Karshe Zaka Neme Shi, A'ah, Ka Fara Rãya Dararen da Suka Rage Tun daga Yau Har Zuwa 'Karshen Ramadãn dan Sãmun Tabbacin Muwãfaqa da Lailatul-Qadr.
══════ ❁✿❁ ═══════
FÃTAN ALKHAIRI.
SUBSCRIBE TELEGRAM CHANNEL:👇
https://t.me/TAMBASIRUNIGERIALIMITED
MUTANE (7) ƳAN ALJANNAH
Manzon Allah ﷺ, yace: *"mutane bakwai Allah yana inuwantar dasu a cikin inuwarsa a ranar da babu wata inuwa face sai inuwarsa"*
📒 Sahih Al-Bukhari (660)
👉🏿 *Shugaba mai adalci*, (shine wanda yake tabbatar da adalci a cikin talakawansa).
👉🏿 *Da matashi wanda ya rayu cikin bautar ubangijinsa (Allah).*
👉🏿 *Da mutumin da zuciyarsa ta ratayu (ta ƙullu ko ta shaƙu) da masallaci.*
👉🏿 *Da mutane biyun da suke soyayya domin Allah, suka haɗu dominsa, kuma suka rabu dominsa.*
👉🏿 *Da mutumin da mace ma'abociyar nasaba da kyawu ta nemeshi*, sai yace, *ni ina jin tsoron Allah.*
👉🏿 *Da mutumin da yayi sadaƙa, ya ɓoyeta*, hagunsa bata san me damansa ta bayar ba.
👉🏿 *Da mutumin da ya tuna Allah shi kaɗai, sai idaniyarsa ta zubar da ƙwalla, (hawaye).*
📒 Sahih Al-Bukhari (660)
.
SUBSCRIBE TELEGRAM CHANNEL:👇https://t.me/TAMBASIRUNIGERIALIMITED
Saturday, 16 April 2022
Friday, 15 April 2022
ALƘUR'ÃNI DA AZUMI SUNA YIN CETO
ALƘUR'ÃNI DA AZUMI SUNA YIN CETO.
-
"A ranar ƙiyamah alƙur'ani da azumi za suyi ceto ga bayi waɗanda suka kasance ma'abotansu ne a wannan duniyar, waɗanda suka ƙarar da rayuwarsu wajen yin ta'ammuli dasu a duniya"
-
"Kowane daga cikinsu zai nemi Allah ta'ala ya bashi ceton dukkanin bawan da ya kasance yana neman kusanci da Allah dominsu, sai Allah buwayi ya basu ceton waɗannan bayin nan-take"
-
"Ruwaya daga Abdullahi ɗan Amru, lallai Manzon Allah ﷺ, yace: azumi da alƙur'ani suna yin ceto ga bawa a ranar ƙiyamah, azumi zai ce: haƙiƙa ya ubangiji, ni na hanashi abinci, da sha'awa da rana, to ka bani ceton sa. alƙur'ani kuma sai yace: haƙiƙa na hanashi yin bacci da daddare, to ka bani ceton sa, sai yace: sai suyi ceton"
Ahmad ne ya ruwaito
Thursday, 14 April 2022
{{NASIHAR RANAR JUMMA'A}} (Hijirah 08-08- 1443)
Yau zamuja hankulan yan uwana musulmi kan lura da ayoyin Allah subahanahu wata'ala,,. Dan uwa kasani cewa baka zama cikin mummunai inbaka tunani da lura kan ayoyin Allah, yar uwa kisan dahaka,,
Meye anfanin zuciyar ka dan uwana da baka tuna Allah da ita, ta lura da ayoyin shi abankasa? Meye anfanin zuciyar ki yar uwa dabakya tuna Allah da ita? Meyesa bazakyi tunani ba,
Kazauna kayi tunani dan uwana kaduba saman nan ya'akayi akaginata, kaduba kasan nan ya'akayi aka shimfidata, ka duba duwatsu da tekunan kaduba canjin dare da rana, kullun sai anyi dare kullun sai anyi rana toh dare da ranan nan suna zuwa kafin kai kuma zaka bar su, lalle yakamata kasan Allah inde kanada hankali, inde kina da lafiyayyen tunani yar uwata,,
Lura da dare da rana da jujjuya al'amura Allah yace ayace ga masu hankali, kai baka cikin masu hankalin ne,? Ke bakya ciki ne yar uwa? Toh meye yasa bakwa tunawa,,. ? Toh siffar bayin Allah mummunai suna lura da tunani akan ayoyin Allah, sbd Allah bai haliice su don ayi wasa ba,,. Bai halicce su ba don kawai ashentake amore, a a ya halicce sune don suzame mana aya mubauta mishi shi kadai,,
Allah yace>>
{{إِنَّ فِي خَلْقِ السَّمَاوَاتِ وَالْأَرْضِ وَاخْتِلَافِ اللَّيْلِ وَالنَّهَارِ لَآيَاتٍ لِّأُولِي الْأَلْبَابِ
Lalle ne, a cikin halittar sammai da ƙasa da sãɓãwar dare da yini akwai ãyõyi ga ma'abũta hankali.
191
الَّذِينَ يَذْكُرُونَ اللَّهَ قِيَامًا وَقُعُودًا وَعَلَىٰ جُنُوبِهِمْ وَيَتَفَكَّرُونَ فِي خَلْقِ السَّمَاوَاتِ وَالْأَرْضِ رَبَّنَا مَا خَلَقْتَ هَٰذَا بَاطِلًا سُبْحَانَكَ فَقِنَا عَذَابَ النَّار
Waɗanda suke ambatar Allah a tsaye da zaune da a kan sãsanninsu, kuma suna tunãni a kan halittar sammai da ƙasa: (suna cewa "Yã Ubangijinmu! Ba Ka halitta wannan a kan banza ba. Tsarki ya tabbata gare ka Sabõda haka Ka tsare mu daga azãbar wuta.}}
Toh yan uwa muke tunawa da lura da ayoyin Allah abankasa, domin samun tabbatuwar imani azukatan mu,,, kar mudauki tunin turawa na kawai Allah yakawomu duniyar nan don mushentake، muyi abunda mukaga dama, duk ko wanda yabiyewa tunanin su, toh baizaiyi kishin Allah ba , bazaiyi kishin Annabi s.a.w ba bazaiyi kishin Addinin musulunci da musulmai ba,, saboda sun lalata mishi tunanin shi,,. Allah yarufamana asiri,,
Yaa Allah kasamu cikin bayinka masu tunawa da lura da Ayoyin ka, yaa ka gafarta mana mu da iyayenmu Baki daya,,yaa Allah ka albarka ci rayuwar mu, yaa Allah ka dauramu kan hanya madedeciya, ameen,
Wednesday, 13 April 2022
Monday, 11 April 2022
Abubuwa biyu basu da riba.
Abubuwa biyu basu da riba.
1 Soyayya ba Aure
2 Aure ba soyayya
.............................
Abubuwa biyu sukan dasa kauna.
1 Kyawawan dabi'u
2 Gaskiya
.............................
Abubuwa biyu kan rusa Abota.
1 Karya
2 Gulma ko rashin yadda
..............................
Abubuwa biyu kan kara kwarjini.
1 Rukon amana
2 Ibada
..............................
Abubuwa biyu nasa kunci.
1 Cin mutuncin manya
2 Kazafi
..............................
Abubuwa biyu nasa farin ciki.
1 Kyautatawa
2 hakuree
.............................
Abubuwa biyu nasa kusanci ga Allah.
1 karatun Qur'ani
2 bin dokokinsa
.................,.............
Abubuwa biyu nasa shedan ya gujeka
1 Ambaton Allah
2 bujirewa son xuciya
..............................
Abubuwa biyu nasa ibada ta karbu
1 tauheedi
2 ikhlassi
..............................
Abubuwa biyu da Allah Yakeso
1 Kyautatawa
2 kyakkyawan hali
......,.......................
Abu biyune yasa na turo sakonnan
1 kasancewa musulmi
2 son da nakewa
musulunci
...........................
Abu biyu nakeso kayi in ka karanta
1 kayi aiki da shi
2 kayi sharing ma abokanka
musulmi zuwa wani group don mu amfana baki daya
Matakai 5 da zaka Sauke Alqur'ani cikin watan Ramadan ⤵️
1= Yadda zaka sauke Alqur'ani a watan Ramadan { Cikin kwanaki 30} Ko wace rana Juz'i Daya:
* Asuba: Shafi 4
* Azahar: Shafi 4
* La'asar: Shafi 4
* Magriba: Shafi 4
* Isha'i: Shafi 4
2= Yadda zaka sauke Alqur'ani a watan Ramadan { Cikin kwanaki 15} Kawace Rana Juz'i 2:
* Asuba: Shafi 8
* Azahar: Shafi 8
* La'asar: Shafi 8
* Magriba: Shafi 8
* Isha'i: Shafi 8
3= Yadda zaka sauke Alqur'ani a watan Ramadan { Cikin kwanaki 12} Kawace Rana Juz'i Biyu da Rabi:
* Asuba: Shafi 10
* Azahar: Shafi 10
* La'asar: Shafi 10
* Magriba: Shafi 10
* Isha'i: Shafi 10
4= Yadda zaka sauke Alqur'ani a watan Ramadan { Cikin kwanaki 10} Kawace Rana Juz'i 3:
* Asuba: Shafi 12
* Azahar: Shafi 12
* La'asar: Shafi 12
* Magriba: Shafi 12
* Isha'i: Shafi 12
Wannan kuma Bangare ne na masu Himma ta gaske.
5= Yadda zaka sauke Alqur'ani a watan Ramadan { Cikin kwanaki 6} Kawace Rana Juz'i 5:
* Asuba: Shafi 20
* Azahar: Shafi 20
* La'asar: Shafi 20
* Magriba: Shafi 20
* Isha'i: Shafi 20
Ku tayani Yada wannan Alkhairi domin bamu san adadin Ladan da Ni da Ku zamu samu ba yayinda wani ya sauke Alqur'ni ta dalilin karanta wannan Jawabi ba.
📝Rubutawa: Dan Uwanku a Musulunci: Muhammad Lawan Bin Musa { Abu- Ja'afar }.
DailyAdhkar
#DailyAdhkar
• Laa 'ilaaha 'illallaahu wahdahu laa shareeka lahu, lahul-mulku wa lahul-hamdu, wa Huwa 'alaa kulli shay'in qadeer — either 100 times or 10 times or 1 time
The Prophet Muhammad (ﷺ) said: "Whoever says:
« لاَ إِلَهَ إِلاَّ اللَّهُ، وَحْدَهُ لاَ شَرِيكَ لَهُ، لَهُ الْمُلْكُ وَلَهُ الْحَمْدُ، وَهْوَ عَلَى كُلِّ شَىْءٍ قَدِيرٌ »
(None has the right to be worshipped except Allah, alone, without any partner, to Him belong all sovereignty and praise, and He is over all things omnipotent)
one hundred times will get the same reward as given for freeing ten slaves; and one hundred good deeds will be written in his accounts, and one hundred sins will be deducted from his accounts, and it (his saying) will be a shield for him from Satan on that day till night, and nobody will be able to do a better deed except the one who does more than he."
📚: Sahih Bukhari 6403
The Prophet Muhammad (ﷺ) said: "He who uttered:
« لاَ إِلَهَ إِلاَّ اللَّهُ، وَحْدَهُ لاَ شَرِيكَ لَهُ، لَهُ الْمُلْكُ وَلَهُ الْحَمْدُ، وَهْوَ عَلَى كُلِّ شَىْءٍ قَدِيرٌ »
ten times, he is like one who freed four slaves from the progeny of Ismail."
📚: Sahih Muslim 2693 (6844)
The Prophet Muhammad (ﷺ) said: "Whoever says:
« لاَ إِلَهَ إِلاَّ اللَّهُ، وَحْدَهُ لاَ شَرِيكَ لَهُ، لَهُ الْمُلْكُ وَلَهُ الْحَمْدُ، وَهْوَ عَلَى كُلِّ شَىْءٍ قَدِيرٌ »
in the morning will have a reward equivalent to that for setting free a slave from among the descendants of Isma'il. He will have ten good deeds recorded for him, ten evil deeds deducted from him, he will be advanced ten degrees, and will be guarded from the satan till the evening. If he says them in the evening, he will have a similar recompense till the morning."
📚: Sunan Abi Dawud 5077 | Sahih
Actions that do not invalidate the Fast During Ramadan*
*Actions that do not invalidate the Fast During Ramadan*
*1) 🔶Eating & Drinking Forgetfully*
Narrated Abu Huraira:
The Prophet (ﷺ) said, *_“If somebody eats or drinks forgetfully then he should complete his fast, for what he has eaten or drunk, has been given to him by Allah.”_*
● [Sahih al-Bukhari 1933]
*2) 🔶Vomiting involuntarily*
📜Narrated Abu Hurairah:
The Prophet (ﷺ) said: *_"if one has a sudden attack of vomiting while one is fasting, no expiation is required of him, but if he vomits intentionally he must make expiation"_*
● [Sunan Abu Dawud 2380]
*3) 🔶Wet Dream*
*_“If a man experiences a wet dream this does not invalidate his fast, because it was involuntary on his part; it is similar to the case when something enters his throat whilst he is sleeping.”_*
● [Al-Mughni by Ibn Qudaamah, vol. 3, p. 22]
*4) 🔶Tasting food (without swallowing it)*
Ibn ‘Abbaas said: *_There is nothing wrong with tasting what is being cooked or whatever._*
● [Narrated by al-Bukhaari in a mu’allaq report]
*5) Medical Purposes under certain conditions*
Enemas, eyedrops, eardrops, tooth extraction and treatment of injuries do not invalidate the fast.
*Medical tablets that are placed under the tongue to treat asthma attacks etc, so long as you avoid swallowing any residue.*
Insertion of anything into the vagina such as pessaries, or a speculum, or the doctor’s fingers for the purpose of medical examination.
Insertion of medical instruments or IUD into the womb.
*Anything that enters the urinary tract of a male or female, such as a catheter tube, or medical scopes, or opaque dyes inserted for the purpose of x-rays, or medicine, or a solution to wash the bladder.*
Fillings, extractions or *cleaning of the teeth, whether with a siwaak or toothbrush, so long as you avoid swallowing anything that reaches the throat.*
Rinsing the mouth, gargling, sprays etc. so long as you avoid swallowing anything that reaches the throat.
*Oxygen or anaesthetic gases, so long as that does not give the patient any kind of nourishment.*
Anything that may enter the body via absorption through the skin, such as creams, poultices, etc.
Insertion of a fine tube via the veins for diagnostic imaging or treatment of the veins of the heart or any part of the body.
*Insertion of a scope through the stomach wall to examine the intestines by means of a surgical operation (laparoscopy).*
Taking samples from the liver or any other part of the body, so long as that is not accompanied by administration of solutions.
*Endoscopy, so long as that is not accompanied by administration of solutions or other substances.*
*Introduction of any medical instruments or materials to the brain or spinal column
ZUWA GA YAR UWA MAI ALBARKA
ZUWA GA YAR UWA MAI ALBARKA
A yayin da kike girki ko aikace aikacenki na gida/kitchen to ki yawaita ambaton Allah Zikiri, Istigfari, Salatin Annabi ko tilawar Alkur'ani, wannan zai taimaka miki aikin yayi sauri ga kuma lada kuma kin ribaci lokacinki, ko sauraron wa'azuka da tafsirin Alkur'ani mai girma.
Sannan ki sani hatta girki idan za kiyi ki tsarkake niyya kiyi domin samun lada, an tambayi Shaykh Saleh Alfauzan a kan: Shin mace tana samun ladan girka abincin bude baki a Ramadhan?
Ya ce: Eh za ta samu lada a kan hakan, domin tana shirya abinci ne ga masu azumi, wannan kuma yana cikin taimakon juna a kan aikin kwarai da taqawa, saboda haka tana samun lada.
Sai dai kuma yar uwa mai albarka a kula kar a shagaltu da girke girke a manta da ibada, ki zama mai tsara lokutanki da ayyukanki farawa daga ayyuka mafiya mahimmanci zuwa ga masu mahimmanci, abubuwan da ba su zama dole ba da masu karancin fa'ida a hakura dasu domin a samu wadataccen lokacin yin ibada.
sannan a kiyaye kar da a yi almubazzaranci.
Jinjina gareku matan kwarai matan kirki, Allah ya saka muku da alkhairi da wadannan dawainiya in sha Allahu Aljannah ita ce makomarku🌷
SUBSCRIBE TELEGRAM CHANNEL:👇
https://t.me/DailyHadithss
[04-11 8:19 AM] +234 805 483 6621: KU KIYAYE AZUMINKU
An ruwaito daga Abu Hurairaih ya ce: Manzon Allah(ﷺ) ya ce: "Wanda bai bar zancen zur ba da aiki dashi, to Allah ba ya bukatar ya bar abincinsa da abin shan sa". Al-Bukhary 1804
Zancen zur shine: Karya da karkata ga barin gaskiya, da aiki da karya, bata da tuhuma.
Cewa Allah ba ya bukatar ya bar abincinsa da abin shan sa: Ma'ana Allah Madaukaki ba ya waiwayan azuminsa kuma ba zai karba daga gareshi ba.
*Ramadan Reminder* You as a man can help them try to help them in cleaning the kitchen or house, fill the bottles in fridge, clean the table, set the table of iftar or Dinner, make juice of iftar, wash the dishes, clean the kitchen etc etc.
Yes man! This is sunnah of our beloved Muhamamd ﷺ to help women in house chores and appreciate their all the efforts and do extra care in Ramadan and free them to do extra ibadaat in Ramadan.
In the month of seeking mercy and forgiveness, providing iftar for someone else is one ideal way to maximise your efforts, and that includes your family! This Ramadan, make it a habit to lighten your mother/wife/sisters role by helping to buy or cook dishes for iftar / Suhoor/ dinner. More often than not, our women are the one cooking daily for the family. In one way or another, if you prepare Iftar or help out with the cooking you can help leave more time for ibadah, rather than spending time cleaning and washing the dishes. Step it up and make it a challenge by cooking a healthy menu for the whole family!
Helping your wife/Mother with household chores is a neglected sunnah. Any man that sees it beneath him or is too arrogant to help his wife/mother around the house is acting against the sunnah and is guilty of chauvinistic behavior.
Aisha, the wife of the Prophet Muhammad (pbuh), was asked, “What did the Prophet (ﷺ) use to do in his house?” She replied, “He used to keep himself busy serving his family (كَانَ يَكُونُ فِي مِهْنَةِ أَهْلِهِ) and when it was the time for prayer he would go for it.” (Bukhari)
Sunday, 10 April 2022
SALLAR DARE (QIYAMULLAILI)!!!
NIGHT PRAYER (QIYAMULLAILI) !!!
.
The Messenger of GOD (ﷺ) said: "Our Lord (ﷻ) sends down every night to the top of the earth, when the last third of the night remains, saying: Who will ask me for an answer, Who will ask me for a loan, Who will Ask forgiveness of my sins and forgive him. ” [Reported by Bukhari and Muslim]
.
At the same time during the holy month of Ramadan there is a lot of enthusiasm and encouragement for good deeds and seeking reward and among them are the Asham prayer and the TAHAJJUD PRAYER.
.
Note that all these prayers are one thing, QIYAMULLAILI, they are all night prayers, the only difference is that Tarawih prayers are performed at the beginning of the night, and Tahajjud is performed at night, but they are all night prayers.
.
And indeed, the night prayer is one of the things that causes a servant to fulfill his desires in this world and the next.
.
Imam Ibn al-Qayyim (may Allah have mercy on him) said: Qiyamullail (night prayer) is one of the most important causes of health, it is one of the things that protects a person from long-term diseases, and it is also one of the things that bring pleasure to the body. soul and mind. ” [Zaadul Ma'ad: 4/227]
.
Whoever performs the night prayer, GOD ()) (SWT) will protect him from the evils of modernity, and it will increase one's self-esteem and glorify this world and the hereafter.
صلاة الليل !!!
.
قال رسول الله صلى الله عليه وسلم: "إن ربنا (ﷻ) ينزل كل ليلة إلى رأس الأرض ، إذا بقي ثلث الليل الأخير فيقول: من يسألني إجابة ، من يسألني. قرض من سيغفر لي ذنوبي ويغفر له. [رواه البخاري ومسلم].
.
في نفس الوقت خلال شهر رمضان المبارك هناك الكثير من الحماس والتشجيع للأعمال الصالحة والسعي للثواب ومن بينها صلاة عشم وصلاة التهجد.
.
علما أن كل هذه الصلوات هي شيء واحد ، القياميلي ، كلها صلاة الليل ، والفرق الوحيد هو أن صلاة التراويح تؤدى في بداية الليل ، والتهجد تؤدى في الليل ، لكنها كلها صلاة الليل.
.
وبالفعل ، فإن صلاة الليل من الأمور التي تجعل العبد يشبع رغباته في الدنيا والآخرة.
.
قال الإمام ابن القيم رحمه الله: (صلاة الليل) من أهم أسباب الصحة ، وهي من الأسباب التي تحمي الإنسان من الأمراض المزمنة ، وهي كذلك. أحد الأشياء التي تسعد الجسد. الروح والعقل. " [زاد المعاد: 4/227]
.
من صلى صلاة الليل ، فإن الله ()) (سبحانه وتعالى) سيحميه من شرور الحداثة ، ويزيد من احترام الذات ، ويمجد الدنيا والآخرة.
.
Manzon ALLAH (Sallallahu Alaihi Wasallam) Ya ce: “Ubangijinmu (ﷻ) yana saukowa kowa ne dare izuwa saman duniya, lokacin da sulusin dare na ƙarshe yayi saura, yana cewa: Waye zai roqe ni bay in amsa masa, Waye, Wayeni zai nemi karinta in gafarta masa zunubansa.” [Bukhari da Muslim suka ruwaito shi]
.
A daidai wannan lokacin da muke ciki a cikin watan Ramadan mai albarka akwai himma da kwaɗaitarwa da jajircewa game da abubuwan alkhairi da neman lada daga ciki akwai akwai SALLAR TARAWIHI (Asham) da kuma SALLUDAR.
.
A lura cewa duka yara Sallolin abu guda ne wato QIYAMULLAILI dukkansu sallar dare ne banbamcinsu kawai shi ne sallar Tarawihi ana yin sa ne a farkon dare, shi kuwa Tahajjud ana yinsa ne can dare amma wamullato sallar dare kar.
.
Kuma ha matasa sallar dare tana daga cikin ayyukan da suke jawowa bawa samun biyan butunsa na duniya da lahira.
.
Imam Ibnul Qayyim (Rahimahullah) Ya ce: “ playeryamullail (Sallar dare) tana daga cikin mafiya amfani sababin tsare lafiya, tana daga cikin abuwan da suke tsare mutum daga wasu zamani masu a dawonishdaki kin da da nishikima j ruhi da kuma zuciya.” [Zadul Ma’ad: 4/227]
.
Duk wanda yake yin Sallar dare, ALLAH (SWT) zai tsare shi daga halaye na zamani, tana kuma kayanwa Mutum kwarjini da kuma tsarin duniya da lahira.
PRIÈRE NOCTURNE (QIYAMULLAILI) !!!
.
Le Messager de DIEU (ﷺ) a dit : « Notre Seigneur (ﷻ) fait descendre chaque nuit sur le sommet de la terre, quand le dernier tiers de la nuit reste, disant : Qui me demandera une réponse, Qui me demandera une réponse. un prêt, qui demandera le pardon de mes péchés et lui pardonnera. » [Rapporté par Bukhari et Muslim]
.
En même temps, pendant le mois sacré du Ramadan, il y a beaucoup d'enthousiasme et d'encouragement pour les bonnes actions et la recherche de récompenses et parmi elles se trouvent la prière Asham et la PRIÈRE TAHAJJUD.
.
Notez que toutes ces prières sont une chose, QIYAMULLAILI, ce sont toutes des prières nocturnes, la seule différence est que les prières de Tarawih sont effectuées au début de la nuit et que Tahajjud est effectué la nuit, mais ce sont toutes des prières nocturnes.
.
Et en effet, la prière nocturne est l'une des choses qui amènent un serviteur à réaliser ses désirs dans ce monde et dans l'autre.
.
L'imam Ibn al-Qayyim (Puisse Allah lui accorder Sa miséricorde) a dit : Qiyamullail (la prière nocturne) est l'une des causes les plus importantes de la santé, c'est l'une des choses qui protège une personne contre les maladies à long terme, et c'est aussi une des choses qui procurent du plaisir au corps, à l'âme et à l'esprit. [Zaadul Ma'ad : 4/227]
.
Celui qui accomplit la prière nocturne, DIEU ()) (SWT) le protégera des maux de la modernité, et cela augmentera son estime de soi et glorifiera ce monde et l'au-delà.
YAYA ALAƘARKI TAKE DA ALƘUR'ÃNI A CIKIN WATAN RAMADANA?
YAYA ALAƘARKI TAKE DA ALƘUR'ÃNI A CIKIN WATAN RAMADANA?
.
🍂 Shin wacce irin alaƙa kika ƙulla da alƙur'ani mai girma a cikin wannan watan na Ramadana mai albarka, kina karantashi ne ko kuma kin nesanta daga gareshi? to kodai a wane hali kike, kada ki kuskura aikace-aikacen cikin gida su haneki daga karantashi ko kuma sauraronsa koda na ƴan lokuta ne.
🍂 Da yawan wasu matan, zaka samesu a zaune a cikin gida, babu abinda suke yi na daga aikace aikace sai kalle-kallen fina-finai kawai, basa karanta alƙur'ani ko sauraronsa, sun nesanta daga gareshi alhalin kuma ana son a kusanceshi musamman ma a cikin wannan watan mai albarka.
🍂 Ki zanto kinyi amfani da rarar lokacin da kike dashi wajen karatun alƙur'ani mai girma a cikin gidanki, koda kin kasance a cikin kicin kike, idan kuwa babu damar karantashi ɗin, to ki daure ki zanto daga cikin masu yawan saurãren ƙira'ar alƙur'ani a cikin wannan watan mai albarka na Ramadan
KADA KAYIWA ANNABI ﷺ ƘARYA!
.
🍃 Yiwa Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ƙarya ba kamar yiwa sauran mutane ƙarya bane
🍃 Abin zai baka mamaki da kuma haushi, musamman akan yanar gizo ta zamani, sai kayi ta ganin ana yaɗa ƙarya akan annabi, ace yace abu kaza alhalin kuwa bai faɗa ba, suna ta bada fatawa ba tare da dalili ba, subhanallah inama dai mutanena sun gane!
🍃 Yiwa Manzon Allah ﷺ ƙarya tamkar halakar da kaine, domin haƙiƙa duk wanda yake yi masa ƙarya da gangan, to lallai yana gina gidan zamansa ne a cikin wuta sakamakon wannan ƙaryar tasa.
🌴Manzon Allah ﷺ yace: *"duk wanda yayi min ƙarya da ganganci, to lallai ya tanadi wurin zamansa daga cikin wuta"*
📒 Jami'i At-tirmiziy (2669)
🍃 Da haka ne zaka gane cewa lallai fa yiwa Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ƙarya ba ƙaramin laifi bane, domin yi masa ƙarya cikin wuta take tunkuɗa mutum matuƙar da gangan yayi ta kuma bai tuba ba.
ME KAKE YI DA AZUMIN NAN?
.
🍂 *Shin mene ne ya kasance aikin yinka wanda kafi baiwa muhimmanci a cikin watan azumin nan?*
👉🏻 Karatun alƙur'ani mai girma, ko kuma na boko, ko kuwa na littattafan musulunci da nazari a cikinsu?
👉🏻 Ko kuma kalle-kallen shirme na fina-finai ka kasance kana aikatawa a cikin wannan watan mai albarka.
👉🏻 Ko kuma dai bacci kawai ka kasance kana baiwa lokacinka.
🍂 Haƙĩƙa babu wani aiki mafi soyuwa a cikin wannan watan na Ramadana fiye da karatun alƙur'ani mai girma, da salloli akan lokutansu, da kuma dukkanin dangogin aiyukan ɗa'a ga Allah swt.
🍂 Kada ka kasance mai ɓata lokacinka a cikin wannan watan mai albarka na Ramadana ta hanyar kalle-kalle da karance-karance marasa amfani a gareka.
🍂 Ka duƙufa wajen aikata ayyukan alkhairi a rayuwarka, musamman ma a cikin wannan watan mai albarka, kada ka banzatar da lokacinka a banza ba tare da ka kasance kana aikata wani kyakkyawan aikin da zai kusantaka da ubangijin taliƙai ba.
Saturday, 9 April 2022
TASKAR ILLIMANTARWA:
TASKAR ILLIMANTARWA:
Azumi yana zamewa mutum kariya daga rinjayar sha'awar varna, saboda hadisin Abdullahi Ɗan Mas'ud رضي الله عنه inda yake cewa, Manzon Allah ﷺ ya ce, “Ya ku taron matasa duk wanda ya sami ikon yin aure daga cikinku to ya yi, domin shi ya fi kaiwa matuqa wajen rintse ido da kiyaye farji, amma wanda duk bai sami ikon yin aure ba, to na hore shi da ya riqa yin azumi, domin azumin zai zame masa garkuwa da kariya.” ()
A ruwayar Abu Sa’id Al-khudri رضي الله عنه ya ce, Manzon Allah ﷺ ya ce, “Duk wanda ya yi azumi saboda Allah ﷻ, to Allah ﷻ zai nisanta fuskarsa daga shiga wuta tsawon tafiyar Shekara saba'in (70).” ()
Haka nan yin azumi saboda Allah ﷻ yana nesanta mutum daga shiga wuta kwatankwacin nisan sama da qasa.
Haka kuma, a wasiyyar da Ma’aiki ﷺ ya bari babu kamar azumi, kamar yadda yazo daga Abu Umamah Al-Bahili رضي الله عنه ya ce, ya Ma’aikin Allah ﷺ ka umarce ni da abin da idan na aikata shi Allah ﷻ zai amfane ni da shi. Sai Manzon Allah ﷺ ya ce, “Ka riqa yin azumi, domin babu kwatankwacinsa. A wata ruwayar kuma ya ce, ka umarce ni da wani abu, sai ya ce, “ka riqa yin azumi, domin babu kamar azumi.”
Wannan ya nuna mana irin falala da darajar da azumi yake da shi.
Azumi yana shigar da mai yin sa Aljannah ta wata qofa da ake ce mata, qofar Rayyan. Saboda hadisin Sahlu Ɗan Sa'ad رضي الله عنه inda yake cewa, Manzon Allah ﷺ ya ce, “Lallai haƙiƙa a cikin qofofin Aljannah akwai wata qofa da ake ce mata Arrayyan, babu mai shiga Aljannah ta cikinta sai masu yin azumi, da farko za a ce ina masu yin azumi? Sai su miqe sai a nuna musu ita, sai su shiga ta cikinta, babu wanda zai shiga aljanna ta wannan qofar sai su, to da zarar sun gama shiga sai a kulle ta, daga nan babu wanda zai shiga ta cikinta bayan su." ()
A wata ruwayar ta Imamul Bukhari a cikin babin siffar 'yan Aljannah ya ce, Ma’aiki ﷺ ya ce, “A cikin Aljanna akwai qofofi guda takwas, a cikinsu akwai wata qofa da ake kiranta Rayyanu, babu mai shiga ta wannan qofa sai mai azumi.”
Abu Hurairah رضي الله عنه ya ce, Manzon Allah ﷺ ya ce, “Wanda ya ciyar da abubuwa guda biyu mabambanta saboda Allah ﷻ, to za a kira shi daga qofofin Aljannah ya shiga, sai a ce, ya kai bawan Allah ﷻ ga alkhairi nan.
Haka kuma duk wanda ya zamo ya fi yawan yin sAllah, sai a kira shi ta qofar sallah, wanda ya fi yin jihadi sai a kira shi ta qofar jihadi.” ()
Wanda ya fi yawan yin azumi sai a kira shi ta qofar Rayyan, wanda ya fi yawan yin sadaka, sai a kira shi ta qofar sadaka.”
Sai sayyidina Abubakar رضي الله عنه ya ce, na ba da Uwata da Ubana don su zama fansarka ya Ma’aikin Allah ﷺ lallai tabbas babu sauran wata damuwa ga wanda aka kira shi ta waɗannan qofofi. Shin za a iya samun wanda za a kira shi ta dukkanin qofofin nan gabaɗayansu? Sai Manzon Allah ﷺ ya ce, “Eh haka ne, ina fata kai ma kana daga cikinsu.” ()
Azumi yana da wasu Xabi'o'i, wanda ya haɗa su zai shiga Aljannah. Manzon Allah ﷺ ya tambayi Sahabbai رضي الله عنهم ya ce, “A cikinku waye ya wayi gari yana azumi?” Sai sayyidina Abubakar رضي الله عنه ya ce, ni ne. Sai ya ce, “Waye a cikinku ya ciyar da wani mabuqaci a yau? Sai sayyidina Abubakar رضي الله عنه ya ce, ni ne. Sai ya ce, “Waye a cikinku ya je dubo mara lafiya a yau?” Sai sayyidina Abubakar رضي الله عنه ya ce, ni ne. Sai Manzon Allah ﷺ ya ce, “Duk wanda waɗannan ɗabi'o'i suka haɗu a gare shi zai shiga Aljannah.” ()
Don haka wanda duk ya haɗa waɗannan ɗabi'u gabaɗayansu, lallai tabbas zai shiga Aljannah.”
Azumi kaffara ne ga zunubai. Huzaifatu Bn Yaman رضي الله عنه ya ruwaito cewa, Manzon Allah ﷺ ya ce: “Jarrabawar mutum da ake yi masa a cikin iyalansa da dukiyarsa da ‘ya‘yansa da maƙwafcinsa, da kuma sallarsa da ya yi da azumin da ya yi da umarni da kyakkyawa da ya yi, da hani da mummuna da ya yi, dukkansu za su zamo dalilin kankarar zunubai a gare shi, da samun wani gwaggwaɓan lada mara iyaka ga duk mai azumi, saboda kasancewar shi mai azumi yana yin haƙuri da juriya na rashin ci da sha, shi ya sa Allah ﷻ zai ba shi lada mara iyaka saboda haƙuri da juriyar da yake yi a halin azumin. Saboda Allah ﷻ yana cewa:
﴿إِنَّمَا يُوَفَّى ٱلصَّٰبِرُونَ أَجْرَهُم بِغَيْرِ حِسَابٍ ﴾ ()
Ma’ana: “lallai (haƙiƙa tabbas) Allah ﷻ yana cika wa masu haƙuri ladansu ba tare da lissafi ba.”
Mai azumi yana da farin ciki guda biyu, na farko: farin cikinsa a duniya yayin da zai yi buɗabaki zai ji yana farin ciki. Na biyu: sai a ranar da zai gamu da Ubangijinsa ﷻ wato zai ga kyakkyawan sakamakon da zai faranta masa rai ita ce darajar shiga Aljannah. Warin bakin mai azumi ya fi turaren Almiski ƙamshi a wurin Allah ﷻ.
Kamar yadda Allah ﷻ Yake faɗa a cikin hadisil ƙudusi, inda yake cewa: “Duk wani aiki da Ɗan Adam zai aikata nasa ne, sai dai azumi shi wannan nawa ne, kuma ni zan ba da sakamakonsa.”
Sannan azumi garkuwa ne, idan dai wani wuni ya zo da ɗayanku yake azumi a cikinsa, to kada ya yi kwarkwasa kada ya yi zolaya, idan kuma wani ya zage shi sai ya ce masa ni ina azumi, sai Ma’aiki ﷺ ya ce, wAllahi warin bakin mai azumi ya fi ƙamshin turaren Almiski.” ()
Azumi zai ceci mai yin sa a gobe ƙiyama.
Haka nan Alqur’ani zai ceci wanda ya shagala da karanta shi a ranar ƙiyama.
Saboda hadisin Abdullahi Ɗan Amru رضي الله عنه wanda Manzon Allah ﷺ yake cewa, “Da azumi da Alqur’ani za su yi ceto ranar Alƙiyama, shi azumi zai ce ya Allah ﷻ na hana shi ci da sha da sha'awar jima'i da rana, ka ba ni ceton sa, shi kuma Alqur’ani zai ce, na hana shi barci da daddare, ka ba ni ceton sa, sai Allah ﷻ Ya karɓi ceton su.” Wato sai Allah ﷻ Ya ba wa azumi da Alqur’ani ceton nasu.
Azumi yana kawar da nunkufurci, da gaba, da ƙiyayya, da waswasi daga cikin ƙirjin mutane. Kamar yadda hadisin mazaunin ƙauyen nan da ya zo daga ƙauye.
Da kuma hadisin Abdullahi Ɗan Abbas رضي الله عنه inda yake cewa, Manzon Allah ﷺ ya ce, “Ka yi azumin watan haƙuri, shi ne azumin watan Ramadan, kuma ka riƙa yin azumin kwana uku a kowane wata domin shi azumi yana tafiyar da mummunan ƙulli daga cikin zuciya.” ()
Azumi ƙofa ce daga cikin ƙofofin alkhairi, kamar yadda ya zo a hadisin Mu'az Bn Jabal wanda Ma’aiki ﷺ yake cewa da shi, “Yanzu ba na nuna maka wata ƙofa daga cikin ƙofofin alkhairi ba?” Sai na ce, gaya min ya Ma’aikin Allah ﷺ, sai ya ce, “Azumi garkuwa ne, sadaƙa kuma tana gusar da saɓo kamar yadda ruwa yake kashe wuta.
Wanda ya mutu da azumi a bakinsa, ana sa ran zai shiga Aljannah kamar yadda ya zo a Hadisin Huzaifata Binil Yaman رضي الله عنه yake cewa, “Wanda ƙarshen kalmarsa ta zamo la'ilaha illAllahu, zai shiga Aljannah.”
Haka nan wanda ya yi azumi a wata rana domin neman yardar Allah ﷻ sai ya mutu yana wannan azumin, to shi ma zai shiga Aljannah.
Haka kuma wanda ya mutu yana cikin ba da sadaka bayan ya gama bayar da sadakar sai ya mutu, kuma ya bayar da sadakar ne domin neman yardar Allah ﷻ, shi ma zai shiga Aljannah.
Allah ﷻ ya tanadi wasu tangama-tangaman gidaje masu benaye a cikin Aljannah, ya kuma tanade su ne ga masu yin azumi, suke kuma ciyarwa, suke tausasa magana, suke yaɗa sallama ga waɗanda suka sani da waɗanda ba su sani ba, suke yin sallah da daddare a lokacin da mutane suke barci.
Saboda hadisin Abu Malik Al’Ashja’i رضي الله عنه inda yake cewa, a cikin Aljannah akwai wasu ɗakuna ana gano cikinsu ta bayansu, kuma ana gano bayansu ta cikinsu.
Wato ana gano mutanen cikinsu ta baya, su kuma na ciki suna gano waɗanda suke wajen ɗakin, ma’ana dai kamar gidan gilashi. Allah ﷻ ya tanade su ne ga wanda yake ciyar da mutane abinci, yake kuma tausasawa a wajen yin magana, yake yawaita azumi, yake yaɗa sallama, da kuma yin sAllah da daddare a lokacin da mutane suke barci.
Ana amsa addu'ar mai azumi wato idan mutum yana azumi Allah ﷻ ba ya mayar da addu'arsa baya, ma’ana ya ƙi karɓa.
Saboda hadisin Abu Hurairah رضي الله عنه inda yake cewa, Manzon Allah ﷺ ya ce, “Mutane uku ba a mayar da addua'rsu shugaba mai adalci, mai azumi har sai ya sha ruwa, da kuma wanda aka zalunta. Allah ﷻ yana ɗaga waɗannan addu'o'in ana ɗaukar su a kan girgije, kuma za a buɗe musu ƙofofin sama. Allah ﷻ Yana cewa: “Na rantse da girmana, da buwayata, sai na taimake ki (ita wannan addu’ar, ko shi wanda aka zalunta) ko bayan wani lokaci ne.” ()
A daidai lokacin da mai azumi zai yi buɗabaki a nan ma ana karɓar addu'a, kamar yadda ya zo a hadisin Abdullahi Ɗan Amru Ɗan As رضي الله عنه ya ce, Manzon Allah ﷺ ya ce, “Lallai shi mai azumi a sanda zai sha ruwa yana da wata addu'a wacce ba a dawo da ita.”
Idan ka ba wa mai azumi abin da zai yi buɗabaki ko ya yi sahur da shi, daidai yake da kamar kai ma ka yi azumin. Manzon Allah ﷺ ne ya faɗi hakan a hadisin Zaidu Bn Khalid Al-Juhani رضي الله عنه inda yake cewa, “Wanda ya ba wa mai azumi abin buɗabaki ko abin sahur, Allah ﷺ zai ba shi lada kwatankwacin azumin wanda ya ciyar ɗin.” ()
Wato idan ya ciyar da mutum goma za a ba shi ladan azumi goma, idan ɗari ya ciyar a ba shi ladan azumi ɗari.
Misali, kamar mai aikin hajji an hana shi ya aske gashin kansa matuƙar dai yana cikin harama, sai dai idan wata larura ce ta same shi a kan, sai ya aske kan sannan ya yi kaffara da yin azumi kamar yadda Allah ﷻ ya ce:
﴿فَإِنْ أُحْصِرْتُمْ فَمَا ٱسْتَيْسَرَ مِنَ ٱلْهَدْىِۖ وَلَا تَحْلِقُوا۟ رُءُوسَكُمْ حَتَّىٰ يَبْلُغَ ٱلْهَدْىُ مَحِلَّهُۥۚ فَمَن كَانَ مِنكُم مَّرِيضًا أَوْ بِهِۦٓ أَذًى مِّن رَّأْسِهِۦ فَفِدْيَةٌ مِّن صِيَامٍ أَوْ صَدَقَةٍ أَوْ نُسُكٍۚ فَإِذَآ أَمِنتُمْ فَمَن تَمَتَّعَ بِٱلْعُمْرَةِ إِلَى ٱلْحَجِّ فَمَا ٱسْتَيْسَرَ مِنَ ٱلْهَدْىِۚ فَمَن لَّمْ يَجِدْ فَصِيَامُ ثَلَٰثَةِ أَيَّامٍ فِى ٱلْحَجِّ وَسَبْعَةٍ إِذَا رَجَعْتُمْۗ تِلْكَ عَشَرَةٌ كَامِلَةٌۗ ذَٰلِكَ لِمَن لَّمْ يَكُنْ أَهْلُهُۥ حَاضِرِى ٱلْمَسْجِدِ ٱلْحَرَامِۚ﴾ ()
Ma’ana: “Idan aka tsare ku, sai ku yanka abin da ya sawwaƙa na hadaya, kada ku aske kawunanku har sai hadayar ta isa wurin yankanta. Wanda ya kasance mara lafiya daga cikinku, ko kuma yana da wani ciwo a kansa da zai sa shi yin aski to sai ya fanshi kansa da yin azumi ko sadaka, ko kuma yanka. Idan kuma kuka aminta cewa ba za a tsare ku ba, to wanda ya yi Tamattu'i da yin umara a cikin watannin aikin hajji, sai ya yanka abin da ya sawwaƙa na hadaya, wanda kuwa bai sami abin yankan ba, sai ya yi azumin kwana uku daga cikin kwanakin aikin hajji, sai ya yi bakwai idan kun komo gida, ya zama goma daidai kenan. Wancan shi ne hukuncin wanda iyalinsa ba su kasance mazauna harami ba.”
Haka nan kuma azumi yana zama kaffara ga wanda ya yi kisan kai bisa kuskure, kamar yadda Allah ﷻ yake cewa:
﴿فَمَن لَّمْ يَجِدْ فَصِيَامُ شَهْرَيْنِ مُتَتَابِعَيْنِ تَوْبَةً مِّنَ ٱللَّهِۗ﴾ ()
Ma’ana: “Wanda bai sami ikon yin hakan ba, sai ya yi azumin wata biyu a
jere a jere, don neman yafewar Allah ﷻ .”
Azumi yana zamowa kaffarar farauta ga wanda ya yi harama da hajji ko umara, kamar yadda Allah ﷻ yake cewa:
﴿يَٰٓأَيُّهَا ٱلَّذِينَ ءَامَنُوا۟ لَا تَقْتُلُوا۟ ٱلصَّيْدَ وَأَنتُمْ حُرُمٌۚ وَمَن قَتَلَهُۥ مِنكُم مُّتَعَمِّدًا فَجَزَآءٌ مِّثْلُ مَا قَتَلَ مِنَ ٱلنَّعَمِ يَحْكُمُ بِهِۦ ذَوَا عَدْلٍ مِّنكُمْ هَدْيًۢا بَٰلِغَ ٱلْكَعْبَةِ أَوْ كَفَّٰرَةٌ طَعَامُ مَسَٰكِينَ أَوْ عَدْلُ ذَٰلِكَ صِيَامًا لِّيَذُوقَ وَبَالَ أَمْرِهِۦۗ عَفَا ٱللَّهُ عَمَّا سَلَفَۚ وَمَنْ عَادَ فَيَنتَقِمُ ٱللَّهُ مِنْهُۗ وَٱللَّهُ عَزِيزٌ ذُو ٱنتِقَامٍ﴾ ()
Ma’ana: “Ya ku waɗanda kuka ba da gaskiya, kada ku kashe abin farauta alhalin kuna cikin harami, duk wanda ya kashe shi daga cikinku da gangan, (zai biya) ramuwar gwargwadon abin da ya kashe na daga dabbobin gida, mutum biyu ne adalai daga cikinku za su yi masa hukunci, ya zamanto hadaya ce mai isa ka'aba, ko kuma ya yi kaffarar ciyar da miskinai, ko kuma ya yi azumi daidai da yawan wuɗannan abin ciyarwar, (an yi masa haka ne) domin ya ɗanɗani sakamakon aikinsa, Allah ﷻ kuma ya yi afuwa ga abin da ya shige, wanda kuma ya sake aikata hakan to Allah ﷻ zai yi masa uquba, Allah ﷻ mabuwayi ne ma'abocin uquba ga wanda ya saɓa masa
Allah ya bamu dacewa.
Friday, 8 April 2022
SHIN ME YAKE KAWO RAUNIN AZZAKARI DA KANKAN CEWAR SA YAKAMATA KOWA YA...
Hanyoyin da zakabi domin rabuwa da matsalar RAUNIN azzakari da kankan cewar gaba inshallah a saurari vidio 👆🤳🙏👋
001 CIGABAN TARIHIN ANNABI MUHAMMADU S A W SADAUKAN TAKAR SA JARUMI NE ...
001 CIGABAN TARIHIN ANNABI MUHAMMADU S A W SADAUKAN TAKAR SA JARUMI NE KARFIN KUDURA NE DASHI SAW
A SAURARI WANNAN VIDIO DOMIN JIN CIKAKKEN BAYANI DAGA BAKIN SHEIKH IBARAHIM MANSUR KADUNA NIGERIA R, T, A
Thursday, 7 April 2022
FALALAR YIN SALLAR ASHAM
___________
Ankarbo daga sayyadi Aliyu dan Abi Dalib
(RTA) yace
Na tambayi manzon Allah (SAW) acikin Falalar
yin sallar Asham Acikin wata Ramadan sai
Manzon Allah (SAW) yace
▓•Wanda yayi Asham adare na farko Awatan
Ramadan mumini yana fita daga cikin laifinsa
kamar yadda mahaifiyarsa ta haifeshi,
▓•Wanda yayi Asham Adarena 2 Allah zai
gafartawa iyayansa,
▓•Wanda yayi Asham Adare na 3 Wani Mala'ika zaikira sunansa a karkashin Al'arshi yace
Anunka aiyukan Alkhairi kuma agafarta
laifukansa,
▓•Wanda yayi Asham Adare na 4 za'a bashi ladan wanda yakaranta Attaura, Injila, zabura,
da Alqur'ani,
▓•Wanda yayi Asham Adare na 5 Za'a bashi ladan yayi
sallah a makka da Madina,
▓•Wanda yayi Asham Adare na 6 za'a bashi
ladan mala'ikun da suke kewaye da Baitul
ma'amuri kuma dukkan dutse da marmara
zasu nemi agafarta masa laifukansa
▓•Wanda yayi Asham Adare na 7 kamar yariski
Annabi musa ne yataimakeshi akashe Fir'auna
da Hamana,
▓•Wanda yayi adare na 8 Allah zaibashi ladan
daya bawa Annabi Ibrahim,
▓•Wanda yayi adare na 9 Kamar ya bautawa Allah ne irin wadda Annabi Muhd (SAW)
Yayiwa Allah,
▓•Wanda yayi adare na 10 Allah zai'azurtashi Da
Alkhairan duniya da lahira,
Wanda yayi adare na 11 zai fita daga duniya
kamar yadda aka haifeshi,
▓•Wanda yayi adare na 12 zaizo ranar Alkiya
yana Amintacce
▓•Wanda yayi adare na 13 Allah zaigina masa
birni Agidan Aljanna,
▓•Wanda yayi adare na 14 Mala'iku zasuzo suyi
masa shaidar yayi sallar Asham baza aimasa hisabiba,
▓•Wanda yayi adare na 15 Mala'iku zasuyi masa
salati da madauka Al'arshi da kursiyu
▓•Wanda yayi adare na 16 Allah zai rubuta
sunansa daga masu kubuta daga wuta,
▓•Wanda yayi adare na 17 za'a bashi lada kamarna dukkan Annabawa,
▓•Wanda yayi adare na 18 wani mala'ika zai
kiransa yace yakai bawan Allah
Allah ya yarda dakai da mahaifanka
▓•Wanda yayi adare na 19 Allah zaidaga
matsayinsa a Aljanna Firdausi,
Ya Allah kabamu rabo duniya da lahira
ءمب
Kuyi Sherin Dan Karuwar Yan Uwa Musulmai
Wednesday, 6 April 2022
KADA KA BAR HARSHENKA YA BUSHE DAGA AMBATON ALLAH (ﷻ)
🇭 🇦 🇩 🇮 🇹 🇭:
KADA KA BAR HARSHENKA YA BUSHE DAGA AMBATON ALLAH (ﷻ)
Hadisi Ya Tabbata Manzon Allah (ﷺ) Yana Cewa:
عن عبد الله بن بسر رضي الله عنه، قال (لما شكا الرجل حاله قال: يا رسول الله! إن شعائر الإسلام قد كثرت عليَّ فأخبرني بأمر أتشبَّثُ به، قال: (لا يزال لسانك رطباً من ذكر الله)
[رواه الترمذي وصححه الألباني]
An Karɓo Daga Abdallahi bn Basr (ra), Yace: Yayin Da Wani Mutum Yazo da Ƙorafi Yace: Ya Manzon Allah (ﷺ)! Lallai Ayyukan Musulunci Sunyi Yawa Agareni, Ka Sanar Dani Wani Abinda Zanyi Riƙo Dashi. Sai Manzon Allah (ﷺ) Yace: “Kada Harshenka Ya Gushe A Jiƙe Daga Ambaton Allah”.
(Tirmizi Ya Ruwaitoshi, Kuma Albani Ya Ingantashi)
Yana daga Cikin Falalar Ambaton Allah, Shine Yanda Manzon Allah (ﷺ) Ya Fifita Ambaton Allah Sama da Duk Abinda Ke Cikin Duniyar Nan.
عن أبي هريرة رضي الله عنه، قال: قال رسول الله صلى الله عليه وسلم: ((لأن أقول سبحان الله، والحمد لله، ولا إله إلا الله، والله أكبر أحبُّ إليَّ ممَّا طلعت عليه الشمس))
(رواه مسلم)
An Karɓo Daga Abi-Hurairah (ra) Yace: Manzon Allah (ﷺ) Yace: “Na Faɗi SUBHANALLAH, WAL HAMDULILLAH, WA LA'ILAHA ILALLLAH, WALLAHU AKBAR, Yafi Soyuwa Gareni Sama da Duk Abinda Rana Ta Fito Akansa”.
(Muslim Ya Ruwaitoshi)
Yana Daga Cikin Fa'idar Zikiri, Yanda Ubangiji (ﷻ) Yayi Alƙawarin Ambaton Wanda Ya Ambaceshi. Wannan Falalar Kaɗai Ta Ubangiji (ﷻ) Zai Tuna Wanda Ya Tunashi Ta Isa Tasa Duk Wani Musulmi Ya Hanu Daga Shagaltuwa Ga Barin Ambaton Allah (ﷻ).
Allah (ﷻ) Yana Cewa:
﴿ فَاذْكُرُونِي أَذْكُرْكُمْ وَاشْكُرُوا لِي وَلَا تَكْفُرُونِ ﴾
[البقرة: ١٥٢]
“Sabõda Haka, Idan Kuka Tuna Ni, Zan Tunã Ku, Kuma Ku Yi Gõdiya Gare Ni, Kuma Kada Ku Butulce Mini”.
(Baƙara: 152)
Sheikhul Islam Ahmad Bn Abdulhalim (rh) Yana Cewa:
(الذكر للقلب مثل الماء للسمك، فكيف يكون حال السمك إذا فارق الماء؟!)
“Ambaton Allah Ga Zuciya Kamar Ruwa Ne Ga Kifi. Yaya Halin Kifi Zai Kasance Idan Ya Rabu da Ruwa?!”
Ibn Aun (rh) Yana Cewa:
(ذكر الناس داء، وذكر الله دواء)
“Ambaton Mutane Cuta Ne, Ambaton Allah Kuma Magani Ne”.
Yahya bn Mu'az (rh) Yana Cewa:
(حادثوا القلوب بذكر الله تعالى، فإنها سريعة الغفلة، فاللسان لا بدَّ له أن يتكلم إما بخيرٍ أو بشـرٍّ أو بأمرٍ مباح، فانظر لنفسك ألا تتكلَّم إلا بما يرضي ربَّك عز وجل وتجده في صحيفتك يوم القيامة، ومن أعظم العقوبات الغفلة عن الذكر)
“Ku Zanta Da Zuciyoyi da Ambaton Allah Maɗaukaki, Domin Tanada Saurin Gafala. Babu Makawa Harshe Sai Yayi Magana; Kodai Zancen Alkhairi Ko Na Sharri Ko Kuma Abinda Yake Na Halas. Ka Dubi Kanka, Kada Kayi Magana Sai Da Abinda Allah Ya Yarda Dashi, Domin Zaka Samu Duk Abinda Ka Furta a Cikin Littafinka Ranar Alƙiyama. Yana Daga Cikin Mafi Girman Uquba, Shine Gafala Daga Ambaton Allah”.
Allah (ﷻ) Yana Cewa:
﴿وَلَا تُطِعْ مَنْ أَغْفَلْنَا قَلْبَهُ عَنْ ذِكْرِنَا وَاتَّبَعَ هَوَاهُ وَكَانَ أَمْرُهُ فُرُطًا﴾
[الكهف: ٢٨]
“Kuma Kada Kabi Wanda Muka Shagaltar Da Zũciyarsa Daga Ambaton Mu, Kuma Ya Bi Son Zuciyarsa, Alhãli Kuwa Al'amarinsa Ya Kasance Yin Ɓarna”.
(Kahfi: 28)
Daga Ƙarshe, Ubangiji (ﷻ) Yana Cewa:
(الَّذِينَ آمَنُوا وَتَطْمَئِنُّ قُلُوبُهُمْ بِذِكْرِ اللَّه أَلا بِذِكْرِ اللَّهِ تَطْمَئِنُّ الْقُلُوبُ)
[سورة الرعد: ٢٨]
“Waɗanda Suka Yi Ĩmãni Kuma Zukãtansu Sukan Natsu Da Ambaton Allah. To, Da Ambaton Allah Zukãta Suke Natsuwa”.
(Ra'ad: 28)
YA ALLAH KA NATSAR DA ZUKATAN MU DA AMBATONKA, KA SANYA MU CIKIN BAYINKA DA ZAKA AMBATO CIKIN DANDAZON MALA'IKUNKA
✍🏽Abu Aysha Al-Maliky
🕌🇦 🇿 🇰 🇦 🇷
AZKAR OF THE DAY
➖➖➖➖➖➖➖➖
🌺 Recite this Azkar in the morning and evening 10 times and get lot of hasnah..
---------------------------------
Bismillahirrahmanirraheem
---------------------------------
🌷 ✦ La ilaha illAllah wahdahu la sharika lahu, lahul-mulk wa lahul-hamd Yuhi wa Yumeet, wa huwa Ala kulli shayin qadir
✦ *لاَ إِلَهَ إِلاَّ اللَّهُ وَحْدَهُ لاَ شَرِيكَ لَهُ لَهُ الْمُلْكُ وَلَهُ الْحَمْدُ يُحْيِي وَيُمِيتُ وَهُوَ عَلَى كُلِّ شَيْءٍ قَدِيرٌ*
✦There is no Lord except Allah , Alone with no partner, to Him belongs the dominion, and to Him is all the praise, He gives life and death, and He has power over all things
✦ : Abu Ayyub Ansari Radi Allahu Anhu narrated that: Rasool Allah Sallallahu Alaihi wasallam said: Whoever says these words ten times in the morning , for every one time Allah subhanahu will write 10 good deeds for him , Will wipe away 10 evil deeds and will raise 10 degrees for him, and these words will be equal for him as he has freed 10 captives ( if anybody say 10 times then this rewards will be ten fold) and it will be his weaopan from the beginning of the day untill the end of the day. and that day nobody will be able to do any deeds which is more better than this and if he say same words in the evening will get same rewards
Al-Silsila-tus-Sahiha-2967-Hasan
DARUSAN RAMADHAN
Darasi na Uku: Hukuncin Azumin Ramadhan
Godiya ta tabbata ga Allah Madaukakin Sarki, wanda ya halicci bayi, kuma ya shar'anta musu hukunce – hukunce da suka dace da rayuwarsu, kuma ya yi tanadin sakamako ga wanda ya kiyaye dokokinsa, da kuma alkawarin narkon azaba ga wanda ya saba masa.
Tsira da amincin Allah su tabbata ga Ma'aikin Allah, Annabi Muhammadu, da iyalan gidansa, da Sahabbansa da wadanda suka bi su da kyautatawa.
Ya ku 'yan'uwana, lallai Azumin watan Ramadhan daya ne daga cikin rukunnan Muslunci da abubuwan da aka gina shi a kansu, Allah ya ce:
{Ya ku wadanda suka yi Imani, an wajabta muku Azumi kamar yadda aka wajabta shi a kan wadanda suka gabace ku, don ku samu tsoron Allah. Ranaku ne kirgaggu, duk wanda ya kasance maras lafiya daga cikinku ko yana halin tafiya to ya kirga a wasu ranakun daban…} [al-Baqara: 183 - 184].
Annabi (saw) ya ce: ((An gina Muslunci a kan abubuwa guda biyar; Shaidawa babu abin bauta sai Allah, kuma Annabi Muhammad ma'aikin Allah ne, da tsayar da Sallah, da ba da Zakka, da aikin Hajji, da Azumin watan Ramadhan)). Sahihul Bukhari (8), Sahihu Muslim (16).
Musulmai sun yi Ijma'i a kan farlancin Azumin watan Ramadhan da kasancewarsa abu sananne wanda babu shakka a kansa a cikin Addinin Muslunci. Kuma sun yi Ijma'i yankakke babu shakka a cikinsa; duk wanda ya yi inkarin wajabcinsa to hakika ya kafirta, za a nemi ya tuba, idan ya tuba, ya yarda da wajabcin Azumin shi kenan, idan kuma ya ki tuba to za a kashe shi a matsayin kafiri, wanda ya yi ridda daga Muslunci. Ba za a yi masa wanka ba, ba za a suturce shi a likkafani ba, ba za a yi masa Sallah ba, ba za a yi masa addu'an neman rahma ba, ba za a bisne shi a makabartan Musulmai ba, kawai za a tona rami ne a can nesa a rufe shi, don kar warinsa ya dami mutane, 'yan'uwansa su cutu.
An farlanta Azumin Ramadhan ne a shekara ta biyu bayan Hijirah, don haka Manzon Allah (saw) ya yi Azumin Ramadhan na tsawon shekaru tara. Kuma farlantawan ya kasance ne a matakai guda biyu:
Na farko: an bayar da zabi tsakanin yin Azumin ko ciyarwa a madadin haka, duk da cewa; Azumin shi ya fi falala.
Mataki na biyu: wajabta Azumin Ramadhan din a kan kowa ba tare da zabi ba. Ya tabbata daga Salama dan Akwa'u (ra) ya ce: ((Lokacin da fadin Allah ya sauka: {Akwai fansan ciyar da miskini a kan wadanda za su iya yin Azumin}, sai ya kasance wanda ya ga dama sai ya sha ruwa ya biya fansa, har sai da Ayar da take bayanta ta sauka, sai ta soke ta)). Sahihul Bukhari (4507), Sahihu Muslim (1145).
Wato yana nufin fadin Allah: {Duk wanda ya halarci watan a cikinku to wajibi ne ya azumce shi. Duk wanda ya kasance maras lafiya ko yana halin tafiya to ya kirga Azumin a wasu ranakun daban}. [al-Baqarah (185)]. Sai Allah ya wajabta Azumin a kan kowa ba tare da zabi ba.
Azumin ba ya wajaba har sai an tabbatar da shigan watan Ramadhan, don haka ba a yin Azumin kafin shigan watan, saboda fadin Annabi (saw):
((Kar dayanku ya gabaci watan Ramadhan da Azumin rana daya ko biyu, sai dai idan mutum ya kasance yana yin wani Azumi na musamman to sai ya azumci ranar)). Bukhari (1914).
Ana yanke hukuncin shigan watan ne da dayan abubuwa guda biyu:
Na farko: ganin jinjirin watan Ramadhan. Allah ya ce:
{Duk wanda ya halarcin watan a cikinku to wajibi ne ya azumce shi}.
Da fadin Annabi (saw): ((Idan kun ga jinjirin watan to ku yi Azumi)). Bukhari (1907) Muslim (1080).
Ba a shardanta dole sai kowane mutum ya gani da kansa ba, a'a, idan mutumin da shaidarsa za ta tabbatar da shigan wata ya ga jinjirin watan shi kenan yin Azumin ya wajaba a kan kowa.
Amma sharadi ne wajen karban shaidar ganin watan sai mai ba da shaidar ya zama Musulmi baligi mai hankali, wanda ake yarda da maganarsa saboda yana da amana, kuma idonsa lafiya kalau yake. Amma kafiri ko yaro ko mahaukaci shigan wata ba ya tabbata da shaidarsu, saboda Hadisin Ibnu Abbas (ra) ya ce: ((Wani bakauye ya zo wajen Annabi (saw) sai ya ce: Lallai na ga jinjirin wata (yana nufin watan Ramadhan), sai Annabi (saw) ya ce: "Shin ka shaida babu abin bauta bisa cancanta sai Allah?" Sai ya ce: Eh.
Ya ce: "Ka shaida Annabi Muhammadu Manzon Allah ne?" Ya ce: Eh. Sai Annabi (saw) ya ce: "Bilal, ka sanar da mutane gobe su yi Azumi")). Abu Dawud (2340), Tirmiziy (691), Nasa'iy (2113), Ibnu Majah (1652).
Haka wanda aka san shi da karya, ko gaggawan ba da labari, ko mai raunin ido to shi ma ba a karban shaidarsa a ganin wata.
Kuma ko da mutum daya ne ya ba da shaidan ganin wata za a karba, saboda Hadisin Abdullahi dan Umar (ra) ya ce: ((Mutane sun nemi ganin jinjirin wata, sai na ba da labari wa Annabi (saw) cewa; na ganshi, sai ya dauki Azumin, kuma ya umurci mutane da su yi Azumin)). Abu Dawud (2342).
Duk wanda ya ga jinjirin wata bisa yakini to wajibi ne ya sanar da shugabannin hukuma, haka watan Shawwal ma. Saboda duk abin da sai da shi wajibi ya cika shi ma wajibi ne.
Amma idan mutum ya ganshi a wajen da yake ba zai iya sanar da shugabanni ba, to shi zai dauki Azumin, sai kuma ya yi iya kokarinsa wajen isar musu gwargwadon iyawarsa.
Idan shugabanni suka sanar da ganin wata a kafafen yada labarai to wajibi ne a yi aiki da sanarwar tasu, wajen shigan watan Ramadhan ko waninsa, saboda sanarwan hukuma hujja ne a Shari'a, ya wajaba a yi aiki da ita. Shi ya sa Annabi (saw) ya umurci Bilal da ya sanar da mutane ganin wata, bayan an tabbatar masa da ganin watan.
Kuma abin lura wajen shigan watan Ramadhan shi ne gani da ido ba lissafi ko amfani da ilimin taurari ba, kamar yadda Hadisai suka nuna cewa; da gani za a yi aiki.
Abu na biyu: ana yin hukunci da shigan watan Ramadhan da cikan watan Sha'aban kwana talatin, saboda wata ba ya wuce kwana talatin, kuma ba ya gaza kwana ishirin da tara. Don haka idan ba a samu tabbacin ganin wata a ranar ishirin da tara ba, imma saboda gajimare ko wani abin daban to sai a cika lissafin watan Sha'aban ya cika kwana talatin, bayan haka sai a yi hukunci da shigan watan Ramadhan. Annabi (saw) ya ce:
((Ku yi Azumi saboda ganin wata, ku sha ruwa (ranar Sallah) saboda ganinsa, amma idan an yi gajimare ya tare muku ganin watan to ku kirga (watan Sha'aban) ya cika kwana talatin)). Bukhari (1909), Muslim (1081).
Allah ya sa mu dace ga bin shiriya, ya ba mu albarkan da ke cikin wannan wata, ya taimake mu a kan yawaita ibada da aiyukan da'a a cikinsa, da nisantar saba masa. Allah ya ba mu tsaro da zaman lafiya a kasarmu, da sauran kasashen Musulmi gaba daya.
Dr. Aliyu Muh'd Sani
Ya ce: "Ka shaida Annabi Muhammadu
Ya ce: "Ka shaida Annabi Muhammadu Manzon Allah ne?" Ya ce: Eh. Sai Annabi (saw) ya ce: "Bilal, ka sanar da mutane gobe su yi Azumi")). Abu Dawud (2340), Tirmiziy (691), Nasa'iy (2113), Ibnu Majah (1652).
Haka wanda aka san shi da karya, ko gaggawan ba da labari, ko mai raunin ido to shi ma ba a karban shaidarsa a ganin wata.
Kuma ko da mutum daya ne ya ba da shaidan ganin wata za a karba, saboda Hadisin Abdullahi dan Umar (ra) ya ce: ((Mutane sun nemi ganin jinjirin wata, sai na ba da labari wa Annabi (saw) cewa; na ganshi, sai ya dauki Azumin, kuma ya umurci mutane da su yi Azumin)). Abu Dawud (2342).
Duk wanda ya ga jinjirin wata bisa yakini to wajibi ne ya sanar da shugabannin hukuma, haka watan Shawwal ma. Saboda duk abin da sai da shi wajibi ya cika shi ma wajibi ne.
Amma idan mutum ya ganshi a wajen da yake ba zai iya sanar da shugabanni ba, to shi zai dauki Azumin, sai kuma ya yi iya kokarinsa wajen isar musu gwargwadon iyawarsa.
Idan shugabanni suka sanar da ganin wata a kafafen yada labarai to wajibi ne a yi aiki da sanarwar tasu, wajen shigan watan Ramadhan ko waninsa, saboda sanarwan hukuma hujja ne a Shari'a, ya wajaba a yi aiki da ita. Shi ya sa Annabi (saw) ya umurci Bilal da ya sanar da mutane ganin wata, bayan an tabbatar masa da ganin watan.
Kuma abin lura wajen shigan watan Ramadhan shi ne gani da ido ba lissafi ko amfani da ilimin taurari ba, kamar yadda Hadisai suka nuna cewa; da gani za a yi aiki.
Abu na biyu: ana yin hukunci da shigan watan Ramadhan da cikan watan Sha'aban kwana talatin, saboda wata ba ya wuce kwana talatin, kuma ba ya gaza kwana ishirin da tara. Don haka idan ba a samu tabbacin ganin wata a ranar ishirin da tara ba, imma saboda gajimare ko wani abin daban to sai a cika lissafin watan Sha'aban ya cika kwana talatin, bayan haka sai a yi hukunci da shigan watan Ramadhan. Annabi (saw) ya ce:
((Ku yi Azumi saboda ganin wata, ku sha ruwa (ranar Sallah) saboda ganinsa, amma idan an yi gajimare ya tare muku ganin watan to ku kirga (watan Sha'aban) ya cika kwana talatin)). Bukhari (1909), Muslim (1081).
Allah ya sa mu dace ga bin shiriya, ya ba mu albarkan da ke cikin wannan wata, ya taimake mu a kan yawaita ibada da aiyukan da'a a cikinsa, da nisantar saba masa. Allah ya ba mu tsaro da zaman lafiya a kasarmu, da sauran kasashen Musulmi gaba daya.
Dr. Aliyu Muh'd Sani
Tuesday, 5 April 2022
*LOKUTAN_AMSAR _ADDU'A*
Don Allah ko bazaka karanta ba katura a groups saboda Al'umma su Amfanq da kai
Kowanne lokaci idan mutum yayi addu'a Allah yana karba.
Sai dai Ubangiji cikin baiwarsa
da falalarsa ya ke'banci wasu
lokuta ya sanya musu albarka
da baiwa fiye da sauran lokutai..
Wadannan lokutan sun hada da:
1. DAREN JUMA'A: Wato ranar
alhamis da dare, da kuma
wunin jumu'ar. Ma'aikin Allah
(alaihis salam) yace "babu wani
bawa wanda zai dace yana addu'a acikinta fache sai Allah
ya amsa masa".
2. WATAN RAMADHAN: gaba
dayansa lokaci ne na amsar
addu'a.
3. LAILATUL QADARI: Shima
lokacin amsar addu'a ne.
4. TSAKAR DARE: Musamman ma sulusin karshensa.. Lokaci ne da Allah yake gwanjon rahamarsa ga bayinsa.
5. LOKACIN DA AKE KIRAN
SALLAH, DA KUMA TSAKANIN
KIRAN SALLAH DA TADA IQAMAH.
6. LOKACIN DA AKA IDAR DA
SALLOLIN FARILLAH.
7. LOKACIN DA AKA GAMA
KARATUN ALQUR'ANI, KO
WA'AZI KO WATA KOYARWA TA
ILMI: Shima lokacin karbar addu'a ne.
8. LOKACIN DA ZAKARA YAYI CHARA. Shima lokacin amsar
addu'a ne.
9. LOKACIN TAFIYA TA ALHERI:
kamar tafiya hajji, sada zumunci, jihadi, ko fatauci.
Shima lokacin amsar addu'a.
10. RANAR ARFA: awannan
ranar, da wanda yake Makkah,
da wanda yake gida, duk Allah
yana amsar addu'arsu.
11. LOKACIN ZUBAN RUWAN
SAMA_ Shima ana amsar addu'a acikinsa.
12. LOKACIN DA AKA TSAIDA
SAHUN YAQIN DAUKAKA
KALMAR ALLAH.. Shima ana
amsar addu'a cikinsa.
13. LOKACIN DA MUTUM YAYI
SUJJADAH. Shima ana amsar
addu'a cikinsa.
14. LOKACIN DA MUTUM YA
FARKA DAGA BARCI: musamman idan mutum ya karanta "sub'hanallah wal'hamdulillah, wa la'ilaha'illal-Lah wallahu akbar" (QAFA 10). Duk abinda ka roka Mustajabah.
Don Allah duk wanda yakaranta yatura a groups 3 tunatarwa ga wanda basuyi like ɗin wannan page suyi like ko following Sabiida faɗakarwa na gaba
ALLAH YA SA MU DACE.. Allah ya
sakawa Malam Da Alheri
Saturday, 2 April 2022
TASKAR ILLIMANTARWA:
Mal. Aminu Ibrahim Daurawa.:
SHIGA WATAN RAMADAN
ANA SHIGA WATAN RAMADAN NE TA HANYOYI GUDA BIYU, BABU TA UKU.
Hanya ta farko: ganin jinjirin wata, shi ganin wata zai iya kasancewa ta fuskoki guda huɗu:
Mutum ɗaya tak ya ga wata shi kadai , wato babu wanda ya gani a duk garin sai shi kadai.
Mutum biyu su gani su kadai a garin gabaɗaya, in banda su babu wanda ya gani.
Mutane da yawa su ga wata a gari ɗaya, sauran garuruwa kuma ba a gani ba. Misali, kamar mutan gari ɗaya, ko unguwa ɗaya, ko layi ɗaya, ko yanki ɗaya, ya zamo su kadai ne suka ga wata.
A ga wata a guraruwa daban-daban a waje daban-daban ko a qasashe daban-daban.
Waɗannan su ne matakan da ake ganin wata ta qarqashinsu.
Idan aka tabbatar da ganin wata ta ɗayan waɗannan matakai, shugabanni suka amince da ganin ta hanyar bin diddigi, sai a ba da sanarwar kowa ya ɗauki azumi.
Hanya ta biyu: Idan ba a ga wata ba, wato babu wanda ya ga wata a gari, ko unguwa, ko qasa, mutum ɗaya ko biyu ko jama'a da yawa, ko kuma an sami wanda ya gani sai dai ba a yarda da ganin nasa ba. Sai a cika lissafin Sha’aban ya zamo kwana talatin (30) daidai.
Ita wannan hanyar ba sai an tsaya neman wanda ya ga wata ba, tun da watan Sha’aban ya cika kwana talatin (30), don haka washegari sai kowa ya tashi da azumi ba sai ya jira umarnin shugaba ba.
Don haka waɗannan su ne hanyoyin da ake shiga watan Ramadan ta cikinsu.
Hujjojin da suka tabbatar da hakan su ne:
Ta farko: hadisin Abdullahi Ɗan Umar رضي الله عنه inda yake cewa, Manzon Allah ﷺ ya ambaci watan Ramadan sai ya ce, “Shi dai wata kwana ashirin da tara (29) ne.”
A wata ruwayar ya ce, “Shi wata haka ne, da haka, da haka.” sai ya haɗa 'yan yatsunsa na dama da hagu, wato yana nufin goma da goma sau biyu ashirin (20) kenan, goma ta uku kuma sai ya lanƙwashe ɗan yatsansa guda ɗaya tara kenan. A wata ruwayar kuma yana cewa, “Shi wata wani lokaci yana yin talatin (30) wani lokaci kuma yana yin ashirin da tara (29), don haka kada ku yi azumi sai kun ga wata, kada ku ajiye sai kun gan shi, idan aka yi muku lullumi, sai ku cika lissafin Sha’aban ya zama talatin (30).” ()
A ruwayar Ummu Salamah kuwa cewa ta yi, Manzon Allah ﷺ ya yi rantsuwa ba zai je wajen iyalinsa ba sai bayan wata guda, to yayin da kwana ashirin da tara (29) suka wuce, sai ya yi sammako ya shiga wajen iyalinsa da daddare, sai wadda ya shiga wajenta ta ce, ya Ma’aikin Allah ﷺ, ai ka rantse cewa ba za ka shiga wajen matanka ba, har tsawon wata guda, ya aka yi kuma ka shigo yanzu? sai ya ce, "Lallai shi wata yakan yi kwana ashirin da tara (29) ne." ()
Shi kuma hadisin Abu Bakarata رضي الله عنه da ya ruwaito daga Ma’aiki ﷺ yana cewa, “Watan Ramadan da watan zulhajji ba sa tauyewa.” ()
Abin da Malamai suka fada a kan ma’anarsa shi ne: Ishaƙ Bn Rahawaihi da Ibn Suwaidin Bn Hubairah sun ce, ma'anar ba sa tauyewa shi ne ba a tauyewa mutum ladan ayyukan da ya aikata a cikinsu ko da kuwa sun tauye a lissafi, ba za su tauye a wajen ba da ladan aiki ba.
Shi kuma Muhammad Bn Sirina ya ce, ba za su haɗu a Shekara kowanensu ya tauye ba.
Shi kuma Imamu Ahmad yana cewa, idan Ramadan ya tauye to Zulhajji zai cika, idan kuma Zulhajji ya tauye to Ramadan zai cika.
Malam Alqasim Bn Muhammad ya ce, na ji Bazzaru yana cewa, waɗannan watanni biyu ba sa tauyewa a Shekara ɗaya a tare.
An ruwaito daga Abu Hurairah رضي الله عنه ya ce, Manzon Allah ﷺ ya ce, “Ku yi azumi in kun ga wata, ku sauke in kun gan shi, idan hazo ko hadari ya rufe muku shi, ku cika kwana talatin (30) na Sha’aban.”
A wata ruwayar ta Muslim ya ce, “In kun ga wata ku yi azumi idan kun gani ku aje, idan girjije ko hadari ya tsare ku, sai ku cika lissafin Sha’aban.”
A wata ruwayar ta Muslim ya ce, “Ku yi azumi don ganin wata, ku ajiye don ganin wata, idan hazo ya rufe muku shi, sai ku qirga talatin (30).” ()
Haka nan hadisin Abdullahi Ɗan Abbas رضي الله عنه ya ce, Manzon Allah ﷺ yana cewa, “Kada ku gabaci wata da yin azumin kwana ɗaya ko biyu, sai dai idan akwai wani azumi da mutum ya saba yi, (sai ya dace da waɗannan ranakun) babu laifi ya yi abinsa, shi asalin wata kwana ashirin da tara ne (29).” Wannan
lafazin Abu Dawud ne.
A taqaice za mu iya cewa hanyoyin ɗaukar azumi guda huɗu ne, kamar yadda muka gabatar.
Na farko shi ne, ganin mutum ɗaya adali, idan hukuma ta gamsu ya zama wajibi ga duk Musulmin da yake wannan garin ya ɗauki wannan azumin.
Dalili hadisin Abdullahi Ɗan Abbas رضي الله عنه inda yake cewa, wani mazaunin qauye ya zo wajen Manzon Allah ﷺ ya ce na ga wata, sai Annabi ﷺ ya ce da shi, “Ka shaida Allah ﷻ shi kaɗai ne ba shi da abokin tarayya, kuma Annabi Muhammadu ﷺ Manzon Allah ﷻ ne? Sai mutumin ya ce eh, sai Manzon Allah ﷺ ya ce, “Ya kai Bilalu je ka ka yi shela ka sanar da mutane cewa su ɗauki azumi gobe.” () Sai dai hadisin yana da rauni, amma malamai sun yi aiki da shi.
Abin nufi yawancin malamai da shi suke aiki cewa za a karɓi shaidar mutum ɗaya adali a gari gabaɗaya.
Wannan shi ne ra'ayin Abdullahi Bn Mubarak, Imamus Shafi'i, da Imamu Ahmad, da Imamu Abu Hanifa, da malaman Kufa, kuma shi ne ra'ayin Jamhuru, sun qArfafi wannan da hadisin Abdullahi Ɗan Umar رضي الله عنه wanda yake cewa, mutane sun duqufa suna duban wata sai Allah ﷻ ya nuna min shi, sai na shaidawa Ma’aiki ﷺ cewa ni na ga wata, sai Ma’aiki Allahi ﷺ ya tashi da azumi kuma ya umarci mutane suka ɗauki azumin.” ()
Sai dai malam Ishak Bn Rahawaihi shi yana ganin ba za a ɗauki azumi da ganin mutum ɗaya ba, sai dai mutum biyu.
Wannan kuma shi ne ra'ayin Imamuna Malik, da Laisu Bn Sa’ad, da Sufyanussauri, da Abdurrahman Al-Auza'i.
Allah ya karɓi ibadar mu.
* * * *
Friday, 1 April 2022
SALLOLIN DARAREN WATAN RAMADAN
SALLOLIN DARAREN WATAN RAMADAN
BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHIM. WA SALLALLAHU ALA MUHAMMADIN WA ALI MUHAMMADIN
.
1• Dare na Farko: Raka'a hudu Fatiha
da Qulhuwa Goma Sha biyar {15}
Kowace Raka'a.
.
2• Dare na Biyu: Raka'a hudu Fatiha
da Inna-Anzalnahu {20} Kowace
Raka'a.
.
3• Dare na Uku: Raka'a {10} Fatiha da
Qulhuwa {50} Kowace Raka'a.
.
4• Dare na Hudu: Raka'a {8} Fatiha da
Inna-Anzalnahu {20} Kowace Raka'a.
.
5• Dare na Biyar: Raka'a {2} Fatiha da
Qulhuwa {50} Kowace Raka'a. bayan Sallama, Allahumma Salli Ala
Muhammadin Wa Ali Muhammadin
{100}.
.
6• Dare na Shida: Raka'a {4} Fatiha da
Tabara Kowace Raka'a.
.
7• Dare na Bakwai: Raka'a {4} Fatiha da Inna-Anzalnahu {13} Kowace
Raka'a.
.
8• Dare na Takwas: Raka'a {2} Fatiha
da Qulhuwa {10} Kowace Raka'a,
Bayan Sallama Subahanallahi {100}
.
9• Dare na Tara: Raka'a {6} Tsakanin Magriba da Isha'i, Fatiha da Kursiyyu
{7} Kowace Raka'a. Bayan Sallama
Salati {50}
.
10• Dare na Goma: Raka'a {20} Fatiha
da Qulhuwa {30}
.
11• Dare na Sha daya: Raka'a {2} Fatiha da Inna'a-adayna Kalkausar
{20}.
.
12• Dare na sha biyu: Raka'a {8}
fatiha da inna-anzalnahu {30}
Kowace Raka'a.
.
13• Dare na sha Uku: Raka'a {4} Fatiha da Qulhuwa {25} Kowace
Raka'a.
.
14• Dare na sha Hudu: Raka'a {6}
Fatiha da Izazul {30} Kowace Raka'a.
.
15• Dare na Sha biyar: Raka'a {4}
Fatiha da Qulhuwa {100} Kowace Raka'a.
.
16• Dare na sha shida: Raka'a {12}
Fatiha da Alhakumu{12} kowace
Raka'a.
.
17• Dare na sha bakwai: Raka'a {2}
Fatiha da Surar data samu, A Raka'a ta farko Fatiha da Qulhuwa {100}
Bayan Sallama La'ilaha Illallahu{100}.
.
18• Dare na sha Takwas: Raka'a {4}
Fatiha da Inna A'adayna {50} Kowace
Raka'a.
.
19• Dare na sha Tara: Raka'a {50} Fatiha da Izazul kowace Raka'a.
.
20• Dare na 20, 21, 22, 23, da 24: A
cikin kowane dare daga wadannan
dararen za'ayi sallah Raka'a {8} da
abin da ya samu na daga karatu.
.
21• Dare na Ashirin da biyar: Raka'a {8} Fatiha da Qulhuwa {10} Kowace
Raka'a.
.
22• Dare na Ashirin da Shida: Raka'a
{8} Fatiha da Qulhuwa {10} Kowace
Raka'a.
.
23• Dare na Ashirin da Bakwai: Raka'a {4} Fatiha da Tabara, idan ba
zaka iya ba to da Qulhuwa {25}
Kowace Raka'a.
.
24• Dare na Ashirin da Takwas:
Raka'a {6} Fatiha da Kursiyyu {10} da
Qulhuwa {10} da Kawthar {10}. Bayan Sallama Salati {10}. Sallar dare
na Ashirin takwas a bisa aka same ta
a hadisai, Raka'a {6} fatiha da
Kursiyyu {10} da Qulhuwa {10} da
Kawthar {10}. Bayan Sallama Salati
{100}
.
25• Dare na Ashirin da Tara: Raka'a
{2} Fatiha da Qulhuwa {20} Kowace
Raka'a.
.
26• Dare na Talatin: Raka'a {12}
Fatiha da Qulhuwa {20} Kowace
Raka'a {8} Bayan Sallama Salati {100}.
Yana daga cikin ayyukan dararen Watan Ramadan Yin Salla Raka'a 1000. Yadda ake yi shi ne: za ka sallaci raka'a 20 a cikin dararen ashirin na watan (wato Goman farko da Goman ta biyu). Kana mai yin raka'a takwas bayan sallar magriba
kafin sallar isha'i, sannan raka'a 12 bayan sallar isha'i. Sannan a kwanakin goman karshe za ka rika yin sallah raka'a 30, raka'a takwas bayan magariba kamar ta farko, sannan raka'a 22 bayan isha'i. idan ka lissafa zaka ga kana da 700 a cikin watan gaba daya don haka saura raka'a 300, su kuma za ka yi su ne a darare na 19 da dare na 23. Wadannan salloli za ka yi raka'a dari-dari na wannan darare ba su shafi talatin din da za ka yi a dararen ba (wato ba za ka ce tunda sallar daya ce ba, kuma na yi talatin to sai na kawo saba'in sun zama dari ke nan. A'a ba haka ba ne, za ka sallaci wadannan ashirin din na daren 19, sannan ka kawo dari. Haka ma dare na 21 da na 23 za ka yi talatin-talatin dinsu kamar yadda aka zayyana a dararen goman karshe, sannan ka kawo dari-dari ka kara.
.
GA LISSAFIN YADDA YAKE:
.
1● Darare Ashirin na farko da raka'a
20×dare 20 = raka'a 400
.
2● Raka'a 30 × dare 10 = raka'a 300
sai ka tara su 400 + 300 = 700
.
3● Raka'a 100 × 3 ) dora 19, 24, 23)
= Raka'a 300, Saika tara da 700 Zai ba ka = 700 + 300 = 1000.
.
IDAN KUMA KA CE DORAWA ZA KA YI, TO LISSAFIN ZAI ZAMA
.
1● Darare 20 din farko kana da
raka'a 400
.
2● Darare 10 karshe kana da raka'a
300
.
3● Dararen 19, 21, 23 kana da 210
(wato idan ya zama ka dora. ne ba ka yi kowacce daban ba)
.
4● Don haka duka sun zama 400 +
300 + 210 = 910 ka ga ba su cika ba.
.
Allah Ya sa Mu Amfana Ilaheeey.
.......copied
Tasirai malam tv
AL falaki tv
Ramli da hisabi tv
Mafarkinka sirrinka tv
Gudun duniya tv
Domin Karin bayani Sai a turo SAKO ta nombarmu ko email zamu baku amsa 👇🤳
taskaasirai@gmail.com
08124763287
08144698283
Subscribe to:
Posts (Atom)
Domin samun mustajaba a kwana 9
Khatimin Allahu Muhammadu idan ka buga adadin Allahu sau Allahu 66×66=4356 sannan sunan Muhammadu sau 92×92=8464 4356+8468=12820 Ana rubu...

-
SIRRIN MALLAKAR MUTUM MACE KO NAMIJI Amman ajitsoron Allah kada kayishi don cuta ko San zuciya ga asirigaskiyane to ga asirin kamar haka ida...