___________
Ankarbo daga sayyadi Aliyu dan Abi Dalib
(RTA) yace
Na tambayi manzon Allah (SAW) acikin Falalar
yin sallar Asham Acikin wata Ramadan sai
Manzon Allah (SAW) yace
▓•Wanda yayi Asham adare na farko Awatan
Ramadan mumini yana fita daga cikin laifinsa
kamar yadda mahaifiyarsa ta haifeshi,
▓•Wanda yayi Asham Adarena 2 Allah zai
gafartawa iyayansa,
▓•Wanda yayi Asham Adare na 3 Wani Mala'ika zaikira sunansa a karkashin Al'arshi yace
Anunka aiyukan Alkhairi kuma agafarta
laifukansa,
▓•Wanda yayi Asham Adare na 4 za'a bashi ladan wanda yakaranta Attaura, Injila, zabura,
da Alqur'ani,
▓•Wanda yayi Asham Adare na 5 Za'a bashi ladan yayi
sallah a makka da Madina,
▓•Wanda yayi Asham Adare na 6 za'a bashi
ladan mala'ikun da suke kewaye da Baitul
ma'amuri kuma dukkan dutse da marmara
zasu nemi agafarta masa laifukansa
▓•Wanda yayi Asham Adare na 7 kamar yariski
Annabi musa ne yataimakeshi akashe Fir'auna
da Hamana,
▓•Wanda yayi adare na 8 Allah zaibashi ladan
daya bawa Annabi Ibrahim,
▓•Wanda yayi adare na 9 Kamar ya bautawa Allah ne irin wadda Annabi Muhd (SAW)
Yayiwa Allah,
▓•Wanda yayi adare na 10 Allah zai'azurtashi Da
Alkhairan duniya da lahira,
Wanda yayi adare na 11 zai fita daga duniya
kamar yadda aka haifeshi,
▓•Wanda yayi adare na 12 zaizo ranar Alkiya
yana Amintacce
▓•Wanda yayi adare na 13 Allah zaigina masa
birni Agidan Aljanna,
▓•Wanda yayi adare na 14 Mala'iku zasuzo suyi
masa shaidar yayi sallar Asham baza aimasa hisabiba,
▓•Wanda yayi adare na 15 Mala'iku zasuyi masa
salati da madauka Al'arshi da kursiyu
▓•Wanda yayi adare na 16 Allah zai rubuta
sunansa daga masu kubuta daga wuta,
▓•Wanda yayi adare na 17 za'a bashi lada kamarna dukkan Annabawa,
▓•Wanda yayi adare na 18 wani mala'ika zai
kiransa yace yakai bawan Allah
Allah ya yarda dakai da mahaifanka
▓•Wanda yayi adare na 19 Allah zaidaga
matsayinsa a Aljanna Firdausi,
Ya Allah kabamu rabo duniya da lahira
ءمب
Kuyi Sherin Dan Karuwar Yan Uwa Musulmai
No comments:
Post a Comment