Monday, 14 March 2022

HANYOYIN DAƊEWA AKAN MACE YIN JIMAI AKAI AKAI

HANYOYIN DAƊEWA AKAN MACE

YIN JIMAI AKAI AKAI

Wato yawan yin jima'i tsakanin ma'aurata na samar da wani yanayi na juriya da daɗewa kafin su kawo (fitar mani). yawan yin jima'i kamar yawan zuwa gidan motsa jiki ne, gwargwadon motsa jininka shine gwargwadon jure wahalar sa da zaka samu. Kuma wannan zai taimaka idan ɗaya daga cikinku baya azalo (withdrawal) domin yawan yin azalo na kara maka tsahon lokaci kafin ka kawo. shiyasa ma yake da kyau ku shawarci juna ya zama ana samar da azalo koda sau daya a sati.

DAUKAR LOKACI MAI TSAHO WAJEN WASANNI

Abinda mafi yawancin mutane suka dauka shine, aiwatar da wasanni kafin saduwa baya da wani tasiri. Sabanin hakan kuwa, yin wasanni kafin saduwa yana bada gudunmawa wajen samarda yanayi na annushuwa tsakanin ma'aurata, sannan yakan kara ma lokacin kasancewa taren tsaho. misali, idan kana daukar mintuna 3 ko 4 kayi komai ka gama tare da matarka ba tare da wasanni ba, idan aka aiwatar da wasanni za'a iya samar da mintuna 8 harma zuwa 10.

FITAR DA SABBIN HIKIMOMIN SADUWA

Idan ka daɗe tare da abokiyar zaman ka, ma'ana kuka kasance na wani lokaci mai tsaho, akwai bukatar ku samar da hikimomi da zasu dinga kara ma kasancewar ku armashi. idan ya zamana kun kasance akan wani salo guda ɗaya na saduwa ko yaushe, zaku kasance cikin gundura da neman canzawa. yana da kyau ku nemi shawarwari daga masana harkar jima'i dan samun sababbin salo da zasu kara muku dadewa tare.

JINKIRIN KAWOWA (INZALI)

Idan mutuminki yana da matsalar inzali da wuri, to ga hanyar da zaki kara matsa dogon zango. lokacin da yake kanki yana sukuwa, ya kusa zuwa gaba sai ki tsayar dashi ta hanyar zare azzakarin daga farjin ki, sai bayan kamar minti biyu sai ki maida masa shi ciki. ya zamana ana samun irin haka kamar sau uku ko huɗu a duk lokacin da kuke saduwa, wannan zai sa ya zama ya kara lokaci akan yadda ya saba, dalilin wannan lattin kawowar da kika masa gwaji akai.

MURZA KARKASHIN AZZAKARIN SA

Duk lokacin da kuke tare ki dinga murza can kasan burar sa, wato kusa da golayensa. hakan yana kara masa dadewa bai kawo ba ya kuma kara ma azzakarin karfi. saidai kada kiyi kuskuren lankwasar da azzakarin a wannan yanayin domin wannan na iya jawo masa lalacewar azzakarin

KE A SAMA SHI A KASA

Wato wannan position yana taimakawa sosai wajen dadewa ba'a kawo ba. domin a haka ko wannen ku zai kasance cikin nishadi ba tare da an taɓa wurare muhimmai ba da zasu sa akawo. yadda akeyi shine, kai zaka kwanta rigingine ita kuma ta hau kanka a zaune tana dan yin gaba da baya.

MAGANI
Daga karshe, yana da kyau ku nemi shawarar masana jima'i domin baku shawarwari da kuma nuna muku irin magungunan da zakuyi amfani dasu da shawo kan matsalar ku. Ba abu ne mai kyau ba ka dinga amfani da magani kawai ba tare da sahalewar likita ba domin zai iya cutar da kai ba tare da kasani ba.

FIFIKON ANNABI AKAN AL'UMMAH (2)

FIFIKON ANNABI AKAN AL'UMMAH (2)


Salati Marashin Farko da Qarshe da tasleemi mafi cikar cika su tabbata bisa Mafi Girman dukkan bayi awajen Allah, Shugabanmu Annabinmu Muhammadu tare da iyalan gidansa Haskaka da Sahabbansa Shiryayyu da dukkan Nagartattun bayinsa har zuwa ranar da Qasa ke fidda nauye-nauyen cikinta. 

8. Yana daga cikin kebantuwar darajarsa cewa shi ka'dai ne Ummiyyi acikin Annabawa (alaihimus salam) wato ba ya karatu ko rubutu amma kuma dukkan wani mai ilimi daga hasken iliminsa ya 'dosana. 

9. Yana daga cikin kebantuwar darajarsa kasancewar acikin littafinsa (Alqur'ani) akwai ayoyin dake shafe hukuncin wasu ayoyin. Amma sauran Annabawa basu samu wannan ba. 

10. Yana daga kebantuwar darajarsa cewa shine Cikamakin dukkan Annabawa da Manzanni (alaihimus salam) Shine mafi darajarsu kuma shine Qarshen aike ﷺ

11. Yana daga kebantuwar darajarsa kasancewar Shari'arsa dawwamammiya ce har zuwa tashin Alqiyamah, Kuma addininsa ya shafe dukkan addinai da shari'o'in da suka zo kafinsa. 

12. Yana daga cikin kebantuwar darajarsa cewa an bashi ayoyin Qarshen suratul Baqarah ne daga wata taska dake Qarkashin Al'arshi. 

13. Yana daga kebantuwar darajarsa cewa shi kadai aka bama Suratul Fatiha wacce ita ce Sab'ul Mathaniy. Kuma ba'a ta'ba bama wani Annabi kafinsa ba. 

14. Yana daga kebantuwar darajarsa cewa an aikoshi ne zuwa ga dukkan mutane baki daya. Bakakensu da fararensu, da larabawa da baibayi, da kuma dukkan Aljanu baki daya. 

15. Yana daga kebantuwar darajarsa kasancewarsa shine wanda yafi dukkan Manzanni yawaicin mabiya. 

16. Yana daga kebantuwar darajarsa cewa bai ta'ba yiwa Allah laifi ba. Kuma duk da haka Allahn ya yafe masa abinda ya gabata da kuma abinda ya jinkirta. 

17. Yana daga kebantuwar darajarsa cewa shi ka'dai Allah ya bama tafkin nan na Alkauthara. Wanda ruwansa yafi Madara haske, yafi zuma zaqi, kuma yafi Qankara sanyi da da'di. 

18. Yana daga kebantuwar darajarsa cewa shi ka'dai ne Annabin da Allah ya aika zuwa ga dukkan Aljanu baki daya. Kuma yaje yayi wa'azi agaresu har ma wasu da yawa sunyi imani dashi daga cikinsu. 

19. Yana daga kebantuwar darajarsa cewa tafkinsa na Alkauthara yafi dukkan tafkunan Annabawa girma da kuma yawan masu sha. 

20. Yana daga kebantuwar darajarsa cewa Allah Madaukakin Sarki ya bashi rundunonin Mala'iku suna tayashi Yaqi a yakokinsa ﷺ

Salati da amincin Allah su tabbata bisa Annabi Muhammadu da iyalan gidansa bisa gwargwadon yawan dukkan Salatai da tasleemai da aka ta'ba yi gareshi


Sunday, 13 March 2022

MATSALAR AZZARI YA KARE QARIN TSAYI DA KAURI

AMFANONIN ZUMUNCI GA DANGI





AMFANONIN ZUMUNCI GA DANGI
منافع صلة الرحم
1. Allah yana farin ciki da mai sada zumunci.
رضا الله تعالي
2. Zumunci na haifar da farin ciki ga mai yin sa.
ادخال السرور علي المومن مع الفرح.
3. Mala'iku na farin ciki ga mai sada zumunci.
فرح الملاءكة.
4. Mai sada zumunci na samun yabo da godiya.
حسن الثناء.
5. Shaiɗan na baƙin ciki ga mai zumunci.
ادخل الغم علي ابليس.
6. Allah na ƙarawa mai sada zumunci tsawon rayuwa.
زيادة في العمر.
7. Allah na sanya albarka a cikin dukiyar mai sada zumunci.
بركة في الرزق.
8. Sada zumunci na sanya farin ciki yayin mutuwa. 
سرور لاموات.
9. Yana samun lada bayan mutuwa saboda 'yan uwa za su riƙa tunawa da shi suna masa addu'a.
زيادة الاجر بعد وفاته لان الاقربين يدعون له.
10. Sada zumunci na ƙara soyayya.
بصلة الرحم تزداد المحبة.
11. Sada zumunci na sanya ƙauna.
تقوي اواصر الالفة بين افراد الاسرة.
12. Ta hanyar sada zumunci ne dangi ke sanin junansu.
بها يتعارف افراد الاسرة.
13. Zumunci na sanya farin ciki da nishaɗi.
تدخل الفرح والسرور في قلوب.
14. Sada zumunci na sanya danƙon ƙauna tsakanin 'yan uwa.
وتقوى العلاقة الاسرية.
15. Sada zumunci na gadar da wanzuwar iyali.
صلة الرحم تحفظ النسل.
16. Sadar da zumunci na sanya mutum ya sami sakamako mai ƙyau wajen Allah.
تسير الحساب امام الله.
17. Sada zumunta na kankare zunubi.
تكفر الذنوب والخطايا.
18. Sada zumunci na zamowa dukiya cikin Aljanna.
صلة الرحم من كنز الجنة.
19. Sada zumunci na ɗaya daga cikin manyan ayyuka na gari.
هىي من أفضل الفضاءل.
Allah ya datar da mu. Ya sanya mu zama masu kusanci ga 'yan uwa da abokan arziƙi.
 Dan Allah inabukatar kayimin addu,a Allah  yasa ingama da duniya lafiya yasa intsallake kyc wassalam jabir mukhtar bello
Copying

SHIN MECECE MUTUWA? (01)





SHIN MECECE MUTUWA? (01)

Mutuwa ita ce rabuwar ruhi da jiki. Wato da zarar ruhinka ya fita daga jikinka to ka mutu kenan. Mutuwa ita ce fitarka daga wani halin zuwa ga wani.. Kuma ita ce fita daga wannan gidan (duniya) zuwa ga wani gidan (lahira). 

Allah da kansa yace Mutuwa Musibah ce.. Acikin littafinsa mai girma inda yake cewa :

"IDAN KUNA TAFIYA A DORON QASA SAI MUSIBAR MUTUWA TA SAMEKU...".

Hakika lallai mutuwa Musibah ce. Amma musibar da tafi ta girma ita ce : GAFALA (WATO RAFKANA) DAGA BARIN AMBATONTA.. Wato Mantawa da tunanin mutuwar. Da kuma rashin yin kyakkyawan tanadin guzuri saboda ranar zuwanta. 

Hakika guzuri ya kamaci mai tafiya. Shi yasa Annabinmu (sallal Laahu alaihi wa aalihi wa sallam) ya wa'azantar damu da irin wa'azin nan mai saurin tsinka zukata, Mai sanya mutum yayi ma kansa hisabi. Kuma yace : "KU YAWAITA AMBATON MAI YANKE JIN-DADI". WATO MUTUWA.

Mutuwa tana zuwa ne babu zato babu tsammani (Bagtatan). Dani mai rubutun, da ku masu karatun nan babu wanda yasan yaushe zai, mutu ? A wanne waje zai, mutu? Da yaya zai mutu? Kuma menene ajalinsa?. 

Wannan ita ce babbar tambayar da bata da amsa.. Kuma babu wani daga cikin mutane wanda ya santa balle ya gaya maka.. Shima bai san tasa ba, balle yasan ta wani. 

Allah yana cewa : "ALLAH AWAJENSA NE SANIN ALQIYAMAH YAKE, KUMA SHI KE SAUKAR DA GIZA-GIZAI KUMA YASAN ABINDA KE CIKIN MAHAIFA. 

"BABU WATA RAI WACCE TASAN ABINDA ZATA TSUWURWURTA GOBE, KUMA BABU WATA RAI DA TASAN AWACCE QASA NE ZATA MUTU".

Hakika mantuwa ko rafkanuwa daga tunanin Mutuwa da 'dacin nan nata, da Kwanciyar Qabari da duhun nan nasa, Da tambayoyin nan na Mala'iku da tsananinta, da ranar Alqiyamah da Tashin hankalin nan nata, da hawan siradi da kaifin nan nasa, Mantuwa daga ambato ko tunanin wadannan yakan sanya zuciya ta bushe har ma alfasha da 'barna su bayyana acikin doron Qasa da teku.. 

Ka sani cewar idan kai mai tuna mutuwa ne, to zaka kasance mai tanadin guzuri domin zuwanta..

Shin yaya sallarka take? Shin kana yinta akan lokacinta, tare da Ikhlasi da tsoron Allah? Shin kana da ilimin sanin tsarki da alwala da hukunce-hukuncen Salla?. In baka dashi mai ya hanaka ka nema?? -- Neman duniya ko? 

Yaya azuminka yake? Shin kana tsaftace idanunka da harshenka ayayin da kake azumi? Shin kana kiyayesu daga kallon haramun, ko furta kalmomon haramun? Ko tunanin aikata sa'bon Allah??.

Shin yaya bin iyayenka yake? Shin kana basu hakkinsu kamar yadda ya dace? Baka 'bata musu rai, baka yi musu tairin kai da girman kai? Shin baka fifita matarka ko abokanka akansu?. 

Yaya sadar da zumuncinka yake? Shin kana hakuri da wautar 'yan uwanka? Shin kana basu hakkinsu? Kana kyautata musu? Kana ziyartarsu?. Ko ko ka biye ma zuciya kana rama mugunta da mugunta?. 

Yaya Mu'amalarka da mutane take? Shin kana sakin fuska ga dukkan Musulmai? Shin kana girmama kowa, kana zaman lafiya da kowa? Shin kana kwatanta adalci da gaskiya da rikon amana acikin kowacce harka ta cikin gidanka da wajen aikinka ko kasuwarka?.

Yaya dukiyarka take? Yaya abincinka da abin shanka yake? Ka tabbatar kan cin halal dinka kana kiyayewa daga haram?. 

Idan akwai matsala yi kokari ka gyara.. Domin mutuwa tana daf da kai.. Mala'ikan mutuwa kullum yana shafa kanka sau saba'in.. Zai iya chafke ruhinka duk sanda aka umurceshi.. 

NASIHA CE DAGA ZAUREN FIQHU



KHAMSUNA HADISI• •HADISI NA 19•

Manzon ALLAH {s.a.w} Yace: Kada kuci da hannun hagu, domin shaiɗan ne keci da hannun hagu.

[Ibn majah]

DARASI:

Ma'ana haramun ne cin wani abinci da hannun hagu.

kuma cin abinci ko sha da hagu yana iya jawowa mutum karɓar sakamakonsa da hagu a ranar Alƙiyama.

Ba ɗabi'ar mumini bace cin abu da hannun hagu.

•HADISI NA 20•

Manzon ALLAH {s.a.w} Yace: Kada ɗayanku yasha abinsha a tsaye.

[Muslim].

DARASI:

Haramun ne shan abinsha a tsaye ko cin wani abu a tsaye.

Saidai mutum ya zauna ko a tsuguna.

Duk wanda yake shan abun sha a tsaye to baya daga cikin mabiya umarnin ALLAH da Manzonsa {s.a.w}.

Ansamu a hadisi cewa Manzon ALLAH {s.a.w} ya sha abin-sha a tsaye, amma idan aka duba waɗannan hadisai sosai za'asamu akwai dalili dayasa ya aikata hakan.

Saboda kiyayewa shine abu mafi alkhairi.

•HADISI NA 21•

Manzon ALLAH {s.a.w} Yace: Kada ɗayanku yayi tafiya da takalmi kafa ɗaya.

[Bukhari da Muslim]

DARASI:

Haramun ne mutum yayi tafiya da takalmi guda ɗaya, sai dai ko ya cire dukka ko kuma ya saka dukka.

Saboda idan takalmin ɗayanku ya tsinke to ya cire dukka kada yayi tafiya acikin takalmi guda ɗaya.

Duk mai aikata haka zai sami kansa acikin fushin ALLAH, kuma sami kansa cikin mummunan hali saboda rashin bin Umarnin ALLAH da manzonsa {s.a.w}.

ALLAH shine mafi sani.

ALLAH kabamu ikon aiki da abinda muka karanta.

ALLAH ka gafarta mana zunubanmu baki ɗaya.
Ameen...


Friday, 11 March 2022

KARATUN TAFIN HANNU 1 AND 14




ASSALAMUALAIKUM YAN UWA ALMAJIRAI MASOYA ANNABI MUHAMMADU S A W MUNA MUKU BARKA DA WANNAN LOKACI YAU  ZAMU CIGABA DA KARATUN TAFIN HANNU 👇🤳🏦 


 

SAHABBAI GOMA DA AKA YIWA BUSHARA DA ALJANNAH




SAHABBAI GOMA DA AKA YIWA BUSHARA DA ALJANNAH 

👉 1. Abubakar Assiddik.
👉 2. Umar Dan Khaddab.
👉 3. Usman Dan Affan.
👉 4. Aliyu Dan Abi Dalib.
👉 5. Dalha Dan Abaidullahi.
👉 6. Zubairu Dan Awwam.
👉 7. Abu Ubaida Dan Jarrah.
👉 8. Abdurrahman Dan Aufu.
👉 9. Sa'adu Dan Abi Wakkas.
👉 10. Sa'idu Dan Zaid.

SHIKA SHIKAN MUSULUNCI GUDA BIYAR 

👉 1. Tauhidi.
👉 2. Sallah.
👉 3. Azumi.
👉 4. Zakkah.
👉 5. Hajji.

SUNAYEN WATANNIN MUSULUNCI : 

👉 1. Almuharram.
👉 2. Safar.
👉 3. Rabi'ul Awwal.
👉 4. Rabi'ul Sani.
👉 5. Jumadal Ula.
👉 6. Jumadal Akhirah.
👉 7. Rajab.
👉 8. Sha'aban.
👉 9. Ramadhan.
👉 10. Shawwal.
👉 11. Zulkidah.
👉 12. Zulhijji.

Ya Allah duk wanda ya taimaka wajen yada wanan ilmin don wasu su amfana; 
Ya Allah ka haskaka rayuwarsa da annurinka, 
Kasa yayi kyakkyawar karshe,
Ka sashi a inuwar Al'arshenka ranar  Alkiyama,
Kuma ka shayar da shi ruwan Alkausara,
Ya Allah ka sa mu  ziyarci juna a gidan Aljannah,
Amin Summa Amin 👏🏻👏👏👏👏👏👏👏

RANAR ALKIYAMA TSAYAWA GABAN ALLAH




Ranar Al Qiyama Kowane Mutum Idan yatashi Abinda yake Qira: Nafsi Nafsi, Annabawa Da Manzanni= Nafsi Nafsi, Iyaye Da Yara= Nafsi Nafsi, Mata Da Maza= Nafsi Nafsi A ranar Shugaba Dayane Shine Annabi Muhammad Rasulullahi {S.a.w} Farkon Tashi Zaice Aina Ummati Aina Ummati Allahu Akabar 'Yan Uwa Kutuna fah yana Da Dangi Amma Daya Tashi Baice Ina Dangi Naba Sai Yace Ina Al'ummata, 'Yan Uwa ko Dan Wannan Bama So Annabi Ba 'Yan Uwa Dan Qaunar Ka/Ki Da Annabi Ka Tura Wannan Zuwa Grp 3 Ko Mutane 3 Ya Allah Ka Samu A Cetan Annabi Muhammadu {S.a.w}. Allah kasa mudace
ALBAKACIN ANNABI S,A,W,   ka tsaya KAKARANTA 
Ya allah ka kare duk wani musulmi daga sharrin.🙏

•Zina
•Luwadi
•Madigo
•Istimina'i
•Sata
•Zalunci
•Munafurci
•Qunchi
•Bashi
•Hasda
•Keta
•Zulama
•Talauchin Duniya da Lahira.

Don alfarmar fiyeyyen halitta Annabi (S,A,W) kadaure kayi share zuwa groups (5)🙏
🔗
🔗 

Ya Allah Ka Karawa Duk wani Musulmin Duniya.

•Lafiya
•Hakuri
•Juriya
•Lafiya
•Karfin imani
•Hankali da Tunani mai kyau
•Mace tagari
•Minji na Gari
•'Ya'ya Na Gari
•Abokan Zama na Kirki
•Arzuki Mai Amfani
•Wadatar Zuci
•Ya Allah Karufawa Duk Wanda Ya
Karanta Wannan Sako Yayi share a groups Yace Ameen
Asiri Duniya da Lahira.

don Allah ☝️ kadaure kayi share zuwa groups 5 👌

SIRRIN BARHATIHIN NA ISMUL AZIM MAI GIRMA




SIRRIN BARHATIHIN NA ISMUL AZIM KADA KA BAWA WANI WANNAN SIRRIN SAI DANKA WANDA YAYI MAKA HIDIMA  SIRRI NE DA AKE BOYE SHI SABODA GIRMAN SHI


 



 

MAULANA SHEHU IBRAHIM NIASSE(R.A) Yana Cewa:-

MAULANA SHEHU IBRAHIM NIASSE(R.A) Yana Cewa:- "Bushewar Zuciya, Itace Mafi Girma a Cikin Bala'i Bayan Kafirci. Akwai Ayyuka Guda 24 Dake Busar Da Zuciya, Wanda SHARI'A Bata Yarda Da Su Ba, 'DARIKA Bata Yarda Dasu Ba, Hakama HAQIQA Bata Yarda Dasu Ba Sune Kamar Haka:- 1 - Mutum Ya Tsaya Akan Zunubi Guda Daya, Yayi Tayi Yana Maimaitawa. 2 - Tsawon Buri, Mutum Ya Zama Bai Wadata Da Abinda ALLAH Ya Bashi Ba. 3 - Yawan Fushi, Ba Akan Tafarkin ALLAH Ba. 4 - Musulmi Ya Riqe Dan'uwansa Musulmi a Zuciya. 5 - Son Duniya Kota Halin Yaya. 6 - Son Girma, Cikin Kowane Hali. 7 - Katsalandan a Harkar Da Ba Ruwanka a Ciki. 8 - Yawan Dariya, Mutum Ya Zama Kamar Wawa. 9 - Yawan Zolayar Mutane. 10 - Jindadi Saboda Abin Duniya, Har Kamanta Da ALLAH Saboda Farin Ciki. 11 - Baqin Ciki, Yayin Da Jindadi Ya Zo Ya Koma. 12 - Gafala Ga Barin Zikirin ALLAH. 13 - Rafkana Ga Barin Tunanin Lahira. 14 - Barin Yin Tunani Akan Sha'anin Wuta. 15 - Barin Yin Tunani Akan Sha'anin Aljannah. 16 - Yawan Yin Firar Banza. 17 - Yawan Yin Abota Da Wawaye. 18 - Da Yawan Cin Haram. 19 - Mugun Cin Abinci. 20 - Da Yawan Janyo Sha'awa. 21 - Yawan Barci 22 - Yawan Tunanin Banza 23 - Qarancin Ambaton ALLAH 24 - Jiji Da Kai KAJI BABBAN LIKITAN ZUCIYA MUN GODE SHEHU! ALLAH YA TSARE MANA ZUCIYOYINMU DAGA BUSHEWA AMEEEN.

Domin samun mustajaba a kwana 9

 Khatimin Allahu Muhammadu  idan ka buga adadin Allahu sau Allahu 66×66=4356 sannan sunan Muhammadu sau  92×92=8464 4356+8468=12820 Ana rubu...