Monday, 11 April 2022
Sunday, 10 April 2022
SALLAR DARE (QIYAMULLAILI)!!!
NIGHT PRAYER (QIYAMULLAILI) !!!
.
The Messenger of GOD (ﷺ) said: "Our Lord (ﷻ) sends down every night to the top of the earth, when the last third of the night remains, saying: Who will ask me for an answer, Who will ask me for a loan, Who will Ask forgiveness of my sins and forgive him. ” [Reported by Bukhari and Muslim]
.
At the same time during the holy month of Ramadan there is a lot of enthusiasm and encouragement for good deeds and seeking reward and among them are the Asham prayer and the TAHAJJUD PRAYER.
.
Note that all these prayers are one thing, QIYAMULLAILI, they are all night prayers, the only difference is that Tarawih prayers are performed at the beginning of the night, and Tahajjud is performed at night, but they are all night prayers.
.
And indeed, the night prayer is one of the things that causes a servant to fulfill his desires in this world and the next.
.
Imam Ibn al-Qayyim (may Allah have mercy on him) said: Qiyamullail (night prayer) is one of the most important causes of health, it is one of the things that protects a person from long-term diseases, and it is also one of the things that bring pleasure to the body. soul and mind. ” [Zaadul Ma'ad: 4/227]
.
Whoever performs the night prayer, GOD ()) (SWT) will protect him from the evils of modernity, and it will increase one's self-esteem and glorify this world and the hereafter.
صلاة الليل !!!
.
قال رسول الله صلى الله عليه وسلم: "إن ربنا (ﷻ) ينزل كل ليلة إلى رأس الأرض ، إذا بقي ثلث الليل الأخير فيقول: من يسألني إجابة ، من يسألني. قرض من سيغفر لي ذنوبي ويغفر له. [رواه البخاري ومسلم].
.
في نفس الوقت خلال شهر رمضان المبارك هناك الكثير من الحماس والتشجيع للأعمال الصالحة والسعي للثواب ومن بينها صلاة عشم وصلاة التهجد.
.
علما أن كل هذه الصلوات هي شيء واحد ، القياميلي ، كلها صلاة الليل ، والفرق الوحيد هو أن صلاة التراويح تؤدى في بداية الليل ، والتهجد تؤدى في الليل ، لكنها كلها صلاة الليل.
.
وبالفعل ، فإن صلاة الليل من الأمور التي تجعل العبد يشبع رغباته في الدنيا والآخرة.
.
قال الإمام ابن القيم رحمه الله: (صلاة الليل) من أهم أسباب الصحة ، وهي من الأسباب التي تحمي الإنسان من الأمراض المزمنة ، وهي كذلك. أحد الأشياء التي تسعد الجسد. الروح والعقل. " [زاد المعاد: 4/227]
.
من صلى صلاة الليل ، فإن الله ()) (سبحانه وتعالى) سيحميه من شرور الحداثة ، ويزيد من احترام الذات ، ويمجد الدنيا والآخرة.
.
Manzon ALLAH (Sallallahu Alaihi Wasallam) Ya ce: “Ubangijinmu (ﷻ) yana saukowa kowa ne dare izuwa saman duniya, lokacin da sulusin dare na ƙarshe yayi saura, yana cewa: Waye zai roqe ni bay in amsa masa, Waye, Wayeni zai nemi karinta in gafarta masa zunubansa.” [Bukhari da Muslim suka ruwaito shi]
.
A daidai wannan lokacin da muke ciki a cikin watan Ramadan mai albarka akwai himma da kwaɗaitarwa da jajircewa game da abubuwan alkhairi da neman lada daga ciki akwai akwai SALLAR TARAWIHI (Asham) da kuma SALLUDAR.
.
A lura cewa duka yara Sallolin abu guda ne wato QIYAMULLAILI dukkansu sallar dare ne banbamcinsu kawai shi ne sallar Tarawihi ana yin sa ne a farkon dare, shi kuwa Tahajjud ana yinsa ne can dare amma wamullato sallar dare kar.
.
Kuma ha matasa sallar dare tana daga cikin ayyukan da suke jawowa bawa samun biyan butunsa na duniya da lahira.
.
Imam Ibnul Qayyim (Rahimahullah) Ya ce: “ playeryamullail (Sallar dare) tana daga cikin mafiya amfani sababin tsare lafiya, tana daga cikin abuwan da suke tsare mutum daga wasu zamani masu a dawonishdaki kin da da nishikima j ruhi da kuma zuciya.” [Zadul Ma’ad: 4/227]
.
Duk wanda yake yin Sallar dare, ALLAH (SWT) zai tsare shi daga halaye na zamani, tana kuma kayanwa Mutum kwarjini da kuma tsarin duniya da lahira.
PRIÈRE NOCTURNE (QIYAMULLAILI) !!!
.
Le Messager de DIEU (ﷺ) a dit : « Notre Seigneur (ﷻ) fait descendre chaque nuit sur le sommet de la terre, quand le dernier tiers de la nuit reste, disant : Qui me demandera une réponse, Qui me demandera une réponse. un prêt, qui demandera le pardon de mes péchés et lui pardonnera. » [Rapporté par Bukhari et Muslim]
.
En même temps, pendant le mois sacré du Ramadan, il y a beaucoup d'enthousiasme et d'encouragement pour les bonnes actions et la recherche de récompenses et parmi elles se trouvent la prière Asham et la PRIÈRE TAHAJJUD.
.
Notez que toutes ces prières sont une chose, QIYAMULLAILI, ce sont toutes des prières nocturnes, la seule différence est que les prières de Tarawih sont effectuées au début de la nuit et que Tahajjud est effectué la nuit, mais ce sont toutes des prières nocturnes.
.
Et en effet, la prière nocturne est l'une des choses qui amènent un serviteur à réaliser ses désirs dans ce monde et dans l'autre.
.
L'imam Ibn al-Qayyim (Puisse Allah lui accorder Sa miséricorde) a dit : Qiyamullail (la prière nocturne) est l'une des causes les plus importantes de la santé, c'est l'une des choses qui protège une personne contre les maladies à long terme, et c'est aussi une des choses qui procurent du plaisir au corps, à l'âme et à l'esprit. [Zaadul Ma'ad : 4/227]
.
Celui qui accomplit la prière nocturne, DIEU ()) (SWT) le protégera des maux de la modernité, et cela augmentera son estime de soi et glorifiera ce monde et l'au-delà.
YAYA ALAƘARKI TAKE DA ALƘUR'ÃNI A CIKIN WATAN RAMADANA?
YAYA ALAƘARKI TAKE DA ALƘUR'ÃNI A CIKIN WATAN RAMADANA?
.
🍂 Shin wacce irin alaƙa kika ƙulla da alƙur'ani mai girma a cikin wannan watan na Ramadana mai albarka, kina karantashi ne ko kuma kin nesanta daga gareshi? to kodai a wane hali kike, kada ki kuskura aikace-aikacen cikin gida su haneki daga karantashi ko kuma sauraronsa koda na ƴan lokuta ne.
🍂 Da yawan wasu matan, zaka samesu a zaune a cikin gida, babu abinda suke yi na daga aikace aikace sai kalle-kallen fina-finai kawai, basa karanta alƙur'ani ko sauraronsa, sun nesanta daga gareshi alhalin kuma ana son a kusanceshi musamman ma a cikin wannan watan mai albarka.
🍂 Ki zanto kinyi amfani da rarar lokacin da kike dashi wajen karatun alƙur'ani mai girma a cikin gidanki, koda kin kasance a cikin kicin kike, idan kuwa babu damar karantashi ɗin, to ki daure ki zanto daga cikin masu yawan saurãren ƙira'ar alƙur'ani a cikin wannan watan mai albarka na Ramadan
KADA KAYIWA ANNABI ﷺ ƘARYA!
.
🍃 Yiwa Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ƙarya ba kamar yiwa sauran mutane ƙarya bane
🍃 Abin zai baka mamaki da kuma haushi, musamman akan yanar gizo ta zamani, sai kayi ta ganin ana yaɗa ƙarya akan annabi, ace yace abu kaza alhalin kuwa bai faɗa ba, suna ta bada fatawa ba tare da dalili ba, subhanallah inama dai mutanena sun gane!
🍃 Yiwa Manzon Allah ﷺ ƙarya tamkar halakar da kaine, domin haƙiƙa duk wanda yake yi masa ƙarya da gangan, to lallai yana gina gidan zamansa ne a cikin wuta sakamakon wannan ƙaryar tasa.
🌴Manzon Allah ﷺ yace: *"duk wanda yayi min ƙarya da ganganci, to lallai ya tanadi wurin zamansa daga cikin wuta"*
📒 Jami'i At-tirmiziy (2669)
🍃 Da haka ne zaka gane cewa lallai fa yiwa Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ƙarya ba ƙaramin laifi bane, domin yi masa ƙarya cikin wuta take tunkuɗa mutum matuƙar da gangan yayi ta kuma bai tuba ba.
ME KAKE YI DA AZUMIN NAN?
.
🍂 *Shin mene ne ya kasance aikin yinka wanda kafi baiwa muhimmanci a cikin watan azumin nan?*
👉🏻 Karatun alƙur'ani mai girma, ko kuma na boko, ko kuwa na littattafan musulunci da nazari a cikinsu?
👉🏻 Ko kuma kalle-kallen shirme na fina-finai ka kasance kana aikatawa a cikin wannan watan mai albarka.
👉🏻 Ko kuma dai bacci kawai ka kasance kana baiwa lokacinka.
🍂 Haƙĩƙa babu wani aiki mafi soyuwa a cikin wannan watan na Ramadana fiye da karatun alƙur'ani mai girma, da salloli akan lokutansu, da kuma dukkanin dangogin aiyukan ɗa'a ga Allah swt.
🍂 Kada ka kasance mai ɓata lokacinka a cikin wannan watan mai albarka na Ramadana ta hanyar kalle-kalle da karance-karance marasa amfani a gareka.
🍂 Ka duƙufa wajen aikata ayyukan alkhairi a rayuwarka, musamman ma a cikin wannan watan mai albarka, kada ka banzatar da lokacinka a banza ba tare da ka kasance kana aikata wani kyakkyawan aikin da zai kusantaka da ubangijin taliƙai ba.
Saturday, 9 April 2022
TASKAR ILLIMANTARWA:
TASKAR ILLIMANTARWA:
Azumi yana zamewa mutum kariya daga rinjayar sha'awar varna, saboda hadisin Abdullahi Ɗan Mas'ud رضي الله عنه inda yake cewa, Manzon Allah ﷺ ya ce, “Ya ku taron matasa duk wanda ya sami ikon yin aure daga cikinku to ya yi, domin shi ya fi kaiwa matuqa wajen rintse ido da kiyaye farji, amma wanda duk bai sami ikon yin aure ba, to na hore shi da ya riqa yin azumi, domin azumin zai zame masa garkuwa da kariya.” ()
A ruwayar Abu Sa’id Al-khudri رضي الله عنه ya ce, Manzon Allah ﷺ ya ce, “Duk wanda ya yi azumi saboda Allah ﷻ, to Allah ﷻ zai nisanta fuskarsa daga shiga wuta tsawon tafiyar Shekara saba'in (70).” ()
Haka nan yin azumi saboda Allah ﷻ yana nesanta mutum daga shiga wuta kwatankwacin nisan sama da qasa.
Haka kuma, a wasiyyar da Ma’aiki ﷺ ya bari babu kamar azumi, kamar yadda yazo daga Abu Umamah Al-Bahili رضي الله عنه ya ce, ya Ma’aikin Allah ﷺ ka umarce ni da abin da idan na aikata shi Allah ﷻ zai amfane ni da shi. Sai Manzon Allah ﷺ ya ce, “Ka riqa yin azumi, domin babu kwatankwacinsa. A wata ruwayar kuma ya ce, ka umarce ni da wani abu, sai ya ce, “ka riqa yin azumi, domin babu kamar azumi.”
Wannan ya nuna mana irin falala da darajar da azumi yake da shi.
Azumi yana shigar da mai yin sa Aljannah ta wata qofa da ake ce mata, qofar Rayyan. Saboda hadisin Sahlu Ɗan Sa'ad رضي الله عنه inda yake cewa, Manzon Allah ﷺ ya ce, “Lallai haƙiƙa a cikin qofofin Aljannah akwai wata qofa da ake ce mata Arrayyan, babu mai shiga Aljannah ta cikinta sai masu yin azumi, da farko za a ce ina masu yin azumi? Sai su miqe sai a nuna musu ita, sai su shiga ta cikinta, babu wanda zai shiga aljanna ta wannan qofar sai su, to da zarar sun gama shiga sai a kulle ta, daga nan babu wanda zai shiga ta cikinta bayan su." ()
A wata ruwayar ta Imamul Bukhari a cikin babin siffar 'yan Aljannah ya ce, Ma’aiki ﷺ ya ce, “A cikin Aljanna akwai qofofi guda takwas, a cikinsu akwai wata qofa da ake kiranta Rayyanu, babu mai shiga ta wannan qofa sai mai azumi.”
Abu Hurairah رضي الله عنه ya ce, Manzon Allah ﷺ ya ce, “Wanda ya ciyar da abubuwa guda biyu mabambanta saboda Allah ﷻ, to za a kira shi daga qofofin Aljannah ya shiga, sai a ce, ya kai bawan Allah ﷻ ga alkhairi nan.
Haka kuma duk wanda ya zamo ya fi yawan yin sAllah, sai a kira shi ta qofar sallah, wanda ya fi yin jihadi sai a kira shi ta qofar jihadi.” ()
Wanda ya fi yawan yin azumi sai a kira shi ta qofar Rayyan, wanda ya fi yawan yin sadaka, sai a kira shi ta qofar sadaka.”
Sai sayyidina Abubakar رضي الله عنه ya ce, na ba da Uwata da Ubana don su zama fansarka ya Ma’aikin Allah ﷺ lallai tabbas babu sauran wata damuwa ga wanda aka kira shi ta waɗannan qofofi. Shin za a iya samun wanda za a kira shi ta dukkanin qofofin nan gabaɗayansu? Sai Manzon Allah ﷺ ya ce, “Eh haka ne, ina fata kai ma kana daga cikinsu.” ()
Azumi yana da wasu Xabi'o'i, wanda ya haɗa su zai shiga Aljannah. Manzon Allah ﷺ ya tambayi Sahabbai رضي الله عنهم ya ce, “A cikinku waye ya wayi gari yana azumi?” Sai sayyidina Abubakar رضي الله عنه ya ce, ni ne. Sai ya ce, “Waye a cikinku ya ciyar da wani mabuqaci a yau? Sai sayyidina Abubakar رضي الله عنه ya ce, ni ne. Sai ya ce, “Waye a cikinku ya je dubo mara lafiya a yau?” Sai sayyidina Abubakar رضي الله عنه ya ce, ni ne. Sai Manzon Allah ﷺ ya ce, “Duk wanda waɗannan ɗabi'o'i suka haɗu a gare shi zai shiga Aljannah.” ()
Don haka wanda duk ya haɗa waɗannan ɗabi'u gabaɗayansu, lallai tabbas zai shiga Aljannah.”
Azumi kaffara ne ga zunubai. Huzaifatu Bn Yaman رضي الله عنه ya ruwaito cewa, Manzon Allah ﷺ ya ce: “Jarrabawar mutum da ake yi masa a cikin iyalansa da dukiyarsa da ‘ya‘yansa da maƙwafcinsa, da kuma sallarsa da ya yi da azumin da ya yi da umarni da kyakkyawa da ya yi, da hani da mummuna da ya yi, dukkansu za su zamo dalilin kankarar zunubai a gare shi, da samun wani gwaggwaɓan lada mara iyaka ga duk mai azumi, saboda kasancewar shi mai azumi yana yin haƙuri da juriya na rashin ci da sha, shi ya sa Allah ﷻ zai ba shi lada mara iyaka saboda haƙuri da juriyar da yake yi a halin azumin. Saboda Allah ﷻ yana cewa:
﴿إِنَّمَا يُوَفَّى ٱلصَّٰبِرُونَ أَجْرَهُم بِغَيْرِ حِسَابٍ ﴾ ()
Ma’ana: “lallai (haƙiƙa tabbas) Allah ﷻ yana cika wa masu haƙuri ladansu ba tare da lissafi ba.”
Mai azumi yana da farin ciki guda biyu, na farko: farin cikinsa a duniya yayin da zai yi buɗabaki zai ji yana farin ciki. Na biyu: sai a ranar da zai gamu da Ubangijinsa ﷻ wato zai ga kyakkyawan sakamakon da zai faranta masa rai ita ce darajar shiga Aljannah. Warin bakin mai azumi ya fi turaren Almiski ƙamshi a wurin Allah ﷻ.
Kamar yadda Allah ﷻ Yake faɗa a cikin hadisil ƙudusi, inda yake cewa: “Duk wani aiki da Ɗan Adam zai aikata nasa ne, sai dai azumi shi wannan nawa ne, kuma ni zan ba da sakamakonsa.”
Sannan azumi garkuwa ne, idan dai wani wuni ya zo da ɗayanku yake azumi a cikinsa, to kada ya yi kwarkwasa kada ya yi zolaya, idan kuma wani ya zage shi sai ya ce masa ni ina azumi, sai Ma’aiki ﷺ ya ce, wAllahi warin bakin mai azumi ya fi ƙamshin turaren Almiski.” ()
Azumi zai ceci mai yin sa a gobe ƙiyama.
Haka nan Alqur’ani zai ceci wanda ya shagala da karanta shi a ranar ƙiyama.
Saboda hadisin Abdullahi Ɗan Amru رضي الله عنه wanda Manzon Allah ﷺ yake cewa, “Da azumi da Alqur’ani za su yi ceto ranar Alƙiyama, shi azumi zai ce ya Allah ﷻ na hana shi ci da sha da sha'awar jima'i da rana, ka ba ni ceton sa, shi kuma Alqur’ani zai ce, na hana shi barci da daddare, ka ba ni ceton sa, sai Allah ﷻ Ya karɓi ceton su.” Wato sai Allah ﷻ Ya ba wa azumi da Alqur’ani ceton nasu.
Azumi yana kawar da nunkufurci, da gaba, da ƙiyayya, da waswasi daga cikin ƙirjin mutane. Kamar yadda hadisin mazaunin ƙauyen nan da ya zo daga ƙauye.
Da kuma hadisin Abdullahi Ɗan Abbas رضي الله عنه inda yake cewa, Manzon Allah ﷺ ya ce, “Ka yi azumin watan haƙuri, shi ne azumin watan Ramadan, kuma ka riƙa yin azumin kwana uku a kowane wata domin shi azumi yana tafiyar da mummunan ƙulli daga cikin zuciya.” ()
Azumi ƙofa ce daga cikin ƙofofin alkhairi, kamar yadda ya zo a hadisin Mu'az Bn Jabal wanda Ma’aiki ﷺ yake cewa da shi, “Yanzu ba na nuna maka wata ƙofa daga cikin ƙofofin alkhairi ba?” Sai na ce, gaya min ya Ma’aikin Allah ﷺ, sai ya ce, “Azumi garkuwa ne, sadaƙa kuma tana gusar da saɓo kamar yadda ruwa yake kashe wuta.
Wanda ya mutu da azumi a bakinsa, ana sa ran zai shiga Aljannah kamar yadda ya zo a Hadisin Huzaifata Binil Yaman رضي الله عنه yake cewa, “Wanda ƙarshen kalmarsa ta zamo la'ilaha illAllahu, zai shiga Aljannah.”
Haka nan wanda ya yi azumi a wata rana domin neman yardar Allah ﷻ sai ya mutu yana wannan azumin, to shi ma zai shiga Aljannah.
Haka kuma wanda ya mutu yana cikin ba da sadaka bayan ya gama bayar da sadakar sai ya mutu, kuma ya bayar da sadakar ne domin neman yardar Allah ﷻ, shi ma zai shiga Aljannah.
Allah ﷻ ya tanadi wasu tangama-tangaman gidaje masu benaye a cikin Aljannah, ya kuma tanade su ne ga masu yin azumi, suke kuma ciyarwa, suke tausasa magana, suke yaɗa sallama ga waɗanda suka sani da waɗanda ba su sani ba, suke yin sallah da daddare a lokacin da mutane suke barci.
Saboda hadisin Abu Malik Al’Ashja’i رضي الله عنه inda yake cewa, a cikin Aljannah akwai wasu ɗakuna ana gano cikinsu ta bayansu, kuma ana gano bayansu ta cikinsu.
Wato ana gano mutanen cikinsu ta baya, su kuma na ciki suna gano waɗanda suke wajen ɗakin, ma’ana dai kamar gidan gilashi. Allah ﷻ ya tanade su ne ga wanda yake ciyar da mutane abinci, yake kuma tausasawa a wajen yin magana, yake yawaita azumi, yake yaɗa sallama, da kuma yin sAllah da daddare a lokacin da mutane suke barci.
Ana amsa addu'ar mai azumi wato idan mutum yana azumi Allah ﷻ ba ya mayar da addu'arsa baya, ma’ana ya ƙi karɓa.
Saboda hadisin Abu Hurairah رضي الله عنه inda yake cewa, Manzon Allah ﷺ ya ce, “Mutane uku ba a mayar da addua'rsu shugaba mai adalci, mai azumi har sai ya sha ruwa, da kuma wanda aka zalunta. Allah ﷻ yana ɗaga waɗannan addu'o'in ana ɗaukar su a kan girgije, kuma za a buɗe musu ƙofofin sama. Allah ﷻ Yana cewa: “Na rantse da girmana, da buwayata, sai na taimake ki (ita wannan addu’ar, ko shi wanda aka zalunta) ko bayan wani lokaci ne.” ()
A daidai lokacin da mai azumi zai yi buɗabaki a nan ma ana karɓar addu'a, kamar yadda ya zo a hadisin Abdullahi Ɗan Amru Ɗan As رضي الله عنه ya ce, Manzon Allah ﷺ ya ce, “Lallai shi mai azumi a sanda zai sha ruwa yana da wata addu'a wacce ba a dawo da ita.”
Idan ka ba wa mai azumi abin da zai yi buɗabaki ko ya yi sahur da shi, daidai yake da kamar kai ma ka yi azumin. Manzon Allah ﷺ ne ya faɗi hakan a hadisin Zaidu Bn Khalid Al-Juhani رضي الله عنه inda yake cewa, “Wanda ya ba wa mai azumi abin buɗabaki ko abin sahur, Allah ﷺ zai ba shi lada kwatankwacin azumin wanda ya ciyar ɗin.” ()
Wato idan ya ciyar da mutum goma za a ba shi ladan azumi goma, idan ɗari ya ciyar a ba shi ladan azumi ɗari.
Misali, kamar mai aikin hajji an hana shi ya aske gashin kansa matuƙar dai yana cikin harama, sai dai idan wata larura ce ta same shi a kan, sai ya aske kan sannan ya yi kaffara da yin azumi kamar yadda Allah ﷻ ya ce:
﴿فَإِنْ أُحْصِرْتُمْ فَمَا ٱسْتَيْسَرَ مِنَ ٱلْهَدْىِۖ وَلَا تَحْلِقُوا۟ رُءُوسَكُمْ حَتَّىٰ يَبْلُغَ ٱلْهَدْىُ مَحِلَّهُۥۚ فَمَن كَانَ مِنكُم مَّرِيضًا أَوْ بِهِۦٓ أَذًى مِّن رَّأْسِهِۦ فَفِدْيَةٌ مِّن صِيَامٍ أَوْ صَدَقَةٍ أَوْ نُسُكٍۚ فَإِذَآ أَمِنتُمْ فَمَن تَمَتَّعَ بِٱلْعُمْرَةِ إِلَى ٱلْحَجِّ فَمَا ٱسْتَيْسَرَ مِنَ ٱلْهَدْىِۚ فَمَن لَّمْ يَجِدْ فَصِيَامُ ثَلَٰثَةِ أَيَّامٍ فِى ٱلْحَجِّ وَسَبْعَةٍ إِذَا رَجَعْتُمْۗ تِلْكَ عَشَرَةٌ كَامِلَةٌۗ ذَٰلِكَ لِمَن لَّمْ يَكُنْ أَهْلُهُۥ حَاضِرِى ٱلْمَسْجِدِ ٱلْحَرَامِۚ﴾ ()
Ma’ana: “Idan aka tsare ku, sai ku yanka abin da ya sawwaƙa na hadaya, kada ku aske kawunanku har sai hadayar ta isa wurin yankanta. Wanda ya kasance mara lafiya daga cikinku, ko kuma yana da wani ciwo a kansa da zai sa shi yin aski to sai ya fanshi kansa da yin azumi ko sadaka, ko kuma yanka. Idan kuma kuka aminta cewa ba za a tsare ku ba, to wanda ya yi Tamattu'i da yin umara a cikin watannin aikin hajji, sai ya yanka abin da ya sawwaƙa na hadaya, wanda kuwa bai sami abin yankan ba, sai ya yi azumin kwana uku daga cikin kwanakin aikin hajji, sai ya yi bakwai idan kun komo gida, ya zama goma daidai kenan. Wancan shi ne hukuncin wanda iyalinsa ba su kasance mazauna harami ba.”
Haka nan kuma azumi yana zama kaffara ga wanda ya yi kisan kai bisa kuskure, kamar yadda Allah ﷻ yake cewa:
﴿فَمَن لَّمْ يَجِدْ فَصِيَامُ شَهْرَيْنِ مُتَتَابِعَيْنِ تَوْبَةً مِّنَ ٱللَّهِۗ﴾ ()
Ma’ana: “Wanda bai sami ikon yin hakan ba, sai ya yi azumin wata biyu a
jere a jere, don neman yafewar Allah ﷻ .”
Azumi yana zamowa kaffarar farauta ga wanda ya yi harama da hajji ko umara, kamar yadda Allah ﷻ yake cewa:
﴿يَٰٓأَيُّهَا ٱلَّذِينَ ءَامَنُوا۟ لَا تَقْتُلُوا۟ ٱلصَّيْدَ وَأَنتُمْ حُرُمٌۚ وَمَن قَتَلَهُۥ مِنكُم مُّتَعَمِّدًا فَجَزَآءٌ مِّثْلُ مَا قَتَلَ مِنَ ٱلنَّعَمِ يَحْكُمُ بِهِۦ ذَوَا عَدْلٍ مِّنكُمْ هَدْيًۢا بَٰلِغَ ٱلْكَعْبَةِ أَوْ كَفَّٰرَةٌ طَعَامُ مَسَٰكِينَ أَوْ عَدْلُ ذَٰلِكَ صِيَامًا لِّيَذُوقَ وَبَالَ أَمْرِهِۦۗ عَفَا ٱللَّهُ عَمَّا سَلَفَۚ وَمَنْ عَادَ فَيَنتَقِمُ ٱللَّهُ مِنْهُۗ وَٱللَّهُ عَزِيزٌ ذُو ٱنتِقَامٍ﴾ ()
Ma’ana: “Ya ku waɗanda kuka ba da gaskiya, kada ku kashe abin farauta alhalin kuna cikin harami, duk wanda ya kashe shi daga cikinku da gangan, (zai biya) ramuwar gwargwadon abin da ya kashe na daga dabbobin gida, mutum biyu ne adalai daga cikinku za su yi masa hukunci, ya zamanto hadaya ce mai isa ka'aba, ko kuma ya yi kaffarar ciyar da miskinai, ko kuma ya yi azumi daidai da yawan wuɗannan abin ciyarwar, (an yi masa haka ne) domin ya ɗanɗani sakamakon aikinsa, Allah ﷻ kuma ya yi afuwa ga abin da ya shige, wanda kuma ya sake aikata hakan to Allah ﷻ zai yi masa uquba, Allah ﷻ mabuwayi ne ma'abocin uquba ga wanda ya saɓa masa
Allah ya bamu dacewa.
Friday, 8 April 2022
SHIN ME YAKE KAWO RAUNIN AZZAKARI DA KANKAN CEWAR SA YAKAMATA KOWA YA...
Hanyoyin da zakabi domin rabuwa da matsalar RAUNIN azzakari da kankan cewar gaba inshallah a saurari vidio 👆🤳🙏👋
001 CIGABAN TARIHIN ANNABI MUHAMMADU S A W SADAUKAN TAKAR SA JARUMI NE ...
001 CIGABAN TARIHIN ANNABI MUHAMMADU S A W SADAUKAN TAKAR SA JARUMI NE KARFIN KUDURA NE DASHI SAW
A SAURARI WANNAN VIDIO DOMIN JIN CIKAKKEN BAYANI DAGA BAKIN SHEIKH IBARAHIM MANSUR KADUNA NIGERIA R, T, A
Thursday, 7 April 2022
FALALAR YIN SALLAR ASHAM
___________
Ankarbo daga sayyadi Aliyu dan Abi Dalib
(RTA) yace
Na tambayi manzon Allah (SAW) acikin Falalar
yin sallar Asham Acikin wata Ramadan sai
Manzon Allah (SAW) yace
▓•Wanda yayi Asham adare na farko Awatan
Ramadan mumini yana fita daga cikin laifinsa
kamar yadda mahaifiyarsa ta haifeshi,
▓•Wanda yayi Asham Adarena 2 Allah zai
gafartawa iyayansa,
▓•Wanda yayi Asham Adare na 3 Wani Mala'ika zaikira sunansa a karkashin Al'arshi yace
Anunka aiyukan Alkhairi kuma agafarta
laifukansa,
▓•Wanda yayi Asham Adare na 4 za'a bashi ladan wanda yakaranta Attaura, Injila, zabura,
da Alqur'ani,
▓•Wanda yayi Asham Adare na 5 Za'a bashi ladan yayi
sallah a makka da Madina,
▓•Wanda yayi Asham Adare na 6 za'a bashi
ladan mala'ikun da suke kewaye da Baitul
ma'amuri kuma dukkan dutse da marmara
zasu nemi agafarta masa laifukansa
▓•Wanda yayi Asham Adare na 7 kamar yariski
Annabi musa ne yataimakeshi akashe Fir'auna
da Hamana,
▓•Wanda yayi adare na 8 Allah zaibashi ladan
daya bawa Annabi Ibrahim,
▓•Wanda yayi adare na 9 Kamar ya bautawa Allah ne irin wadda Annabi Muhd (SAW)
Yayiwa Allah,
▓•Wanda yayi adare na 10 Allah zai'azurtashi Da
Alkhairan duniya da lahira,
Wanda yayi adare na 11 zai fita daga duniya
kamar yadda aka haifeshi,
▓•Wanda yayi adare na 12 zaizo ranar Alkiya
yana Amintacce
▓•Wanda yayi adare na 13 Allah zaigina masa
birni Agidan Aljanna,
▓•Wanda yayi adare na 14 Mala'iku zasuzo suyi
masa shaidar yayi sallar Asham baza aimasa hisabiba,
▓•Wanda yayi adare na 15 Mala'iku zasuyi masa
salati da madauka Al'arshi da kursiyu
▓•Wanda yayi adare na 16 Allah zai rubuta
sunansa daga masu kubuta daga wuta,
▓•Wanda yayi adare na 17 za'a bashi lada kamarna dukkan Annabawa,
▓•Wanda yayi adare na 18 wani mala'ika zai
kiransa yace yakai bawan Allah
Allah ya yarda dakai da mahaifanka
▓•Wanda yayi adare na 19 Allah zaidaga
matsayinsa a Aljanna Firdausi,
Ya Allah kabamu rabo duniya da lahira
ءمب
Kuyi Sherin Dan Karuwar Yan Uwa Musulmai
Wednesday, 6 April 2022
KADA KA BAR HARSHENKA YA BUSHE DAGA AMBATON ALLAH (ﷻ)
🇭 🇦 🇩 🇮 🇹 🇭:
KADA KA BAR HARSHENKA YA BUSHE DAGA AMBATON ALLAH (ﷻ)
Hadisi Ya Tabbata Manzon Allah (ﷺ) Yana Cewa:
عن عبد الله بن بسر رضي الله عنه، قال (لما شكا الرجل حاله قال: يا رسول الله! إن شعائر الإسلام قد كثرت عليَّ فأخبرني بأمر أتشبَّثُ به، قال: (لا يزال لسانك رطباً من ذكر الله)
[رواه الترمذي وصححه الألباني]
An Karɓo Daga Abdallahi bn Basr (ra), Yace: Yayin Da Wani Mutum Yazo da Ƙorafi Yace: Ya Manzon Allah (ﷺ)! Lallai Ayyukan Musulunci Sunyi Yawa Agareni, Ka Sanar Dani Wani Abinda Zanyi Riƙo Dashi. Sai Manzon Allah (ﷺ) Yace: “Kada Harshenka Ya Gushe A Jiƙe Daga Ambaton Allah”.
(Tirmizi Ya Ruwaitoshi, Kuma Albani Ya Ingantashi)
Yana daga Cikin Falalar Ambaton Allah, Shine Yanda Manzon Allah (ﷺ) Ya Fifita Ambaton Allah Sama da Duk Abinda Ke Cikin Duniyar Nan.
عن أبي هريرة رضي الله عنه، قال: قال رسول الله صلى الله عليه وسلم: ((لأن أقول سبحان الله، والحمد لله، ولا إله إلا الله، والله أكبر أحبُّ إليَّ ممَّا طلعت عليه الشمس))
(رواه مسلم)
An Karɓo Daga Abi-Hurairah (ra) Yace: Manzon Allah (ﷺ) Yace: “Na Faɗi SUBHANALLAH, WAL HAMDULILLAH, WA LA'ILAHA ILALLLAH, WALLAHU AKBAR, Yafi Soyuwa Gareni Sama da Duk Abinda Rana Ta Fito Akansa”.
(Muslim Ya Ruwaitoshi)
Yana Daga Cikin Fa'idar Zikiri, Yanda Ubangiji (ﷻ) Yayi Alƙawarin Ambaton Wanda Ya Ambaceshi. Wannan Falalar Kaɗai Ta Ubangiji (ﷻ) Zai Tuna Wanda Ya Tunashi Ta Isa Tasa Duk Wani Musulmi Ya Hanu Daga Shagaltuwa Ga Barin Ambaton Allah (ﷻ).
Allah (ﷻ) Yana Cewa:
﴿ فَاذْكُرُونِي أَذْكُرْكُمْ وَاشْكُرُوا لِي وَلَا تَكْفُرُونِ ﴾
[البقرة: ١٥٢]
“Sabõda Haka, Idan Kuka Tuna Ni, Zan Tunã Ku, Kuma Ku Yi Gõdiya Gare Ni, Kuma Kada Ku Butulce Mini”.
(Baƙara: 152)
Sheikhul Islam Ahmad Bn Abdulhalim (rh) Yana Cewa:
(الذكر للقلب مثل الماء للسمك، فكيف يكون حال السمك إذا فارق الماء؟!)
“Ambaton Allah Ga Zuciya Kamar Ruwa Ne Ga Kifi. Yaya Halin Kifi Zai Kasance Idan Ya Rabu da Ruwa?!”
Ibn Aun (rh) Yana Cewa:
(ذكر الناس داء، وذكر الله دواء)
“Ambaton Mutane Cuta Ne, Ambaton Allah Kuma Magani Ne”.
Yahya bn Mu'az (rh) Yana Cewa:
(حادثوا القلوب بذكر الله تعالى، فإنها سريعة الغفلة، فاللسان لا بدَّ له أن يتكلم إما بخيرٍ أو بشـرٍّ أو بأمرٍ مباح، فانظر لنفسك ألا تتكلَّم إلا بما يرضي ربَّك عز وجل وتجده في صحيفتك يوم القيامة، ومن أعظم العقوبات الغفلة عن الذكر)
“Ku Zanta Da Zuciyoyi da Ambaton Allah Maɗaukaki, Domin Tanada Saurin Gafala. Babu Makawa Harshe Sai Yayi Magana; Kodai Zancen Alkhairi Ko Na Sharri Ko Kuma Abinda Yake Na Halas. Ka Dubi Kanka, Kada Kayi Magana Sai Da Abinda Allah Ya Yarda Dashi, Domin Zaka Samu Duk Abinda Ka Furta a Cikin Littafinka Ranar Alƙiyama. Yana Daga Cikin Mafi Girman Uquba, Shine Gafala Daga Ambaton Allah”.
Allah (ﷻ) Yana Cewa:
﴿وَلَا تُطِعْ مَنْ أَغْفَلْنَا قَلْبَهُ عَنْ ذِكْرِنَا وَاتَّبَعَ هَوَاهُ وَكَانَ أَمْرُهُ فُرُطًا﴾
[الكهف: ٢٨]
“Kuma Kada Kabi Wanda Muka Shagaltar Da Zũciyarsa Daga Ambaton Mu, Kuma Ya Bi Son Zuciyarsa, Alhãli Kuwa Al'amarinsa Ya Kasance Yin Ɓarna”.
(Kahfi: 28)
Daga Ƙarshe, Ubangiji (ﷻ) Yana Cewa:
(الَّذِينَ آمَنُوا وَتَطْمَئِنُّ قُلُوبُهُمْ بِذِكْرِ اللَّه أَلا بِذِكْرِ اللَّهِ تَطْمَئِنُّ الْقُلُوبُ)
[سورة الرعد: ٢٨]
“Waɗanda Suka Yi Ĩmãni Kuma Zukãtansu Sukan Natsu Da Ambaton Allah. To, Da Ambaton Allah Zukãta Suke Natsuwa”.
(Ra'ad: 28)
YA ALLAH KA NATSAR DA ZUKATAN MU DA AMBATONKA, KA SANYA MU CIKIN BAYINKA DA ZAKA AMBATO CIKIN DANDAZON MALA'IKUNKA
✍🏽Abu Aysha Al-Maliky
🕌🇦 🇿 🇰 🇦 🇷
AZKAR OF THE DAY
➖➖➖➖➖➖➖➖
🌺 Recite this Azkar in the morning and evening 10 times and get lot of hasnah..
---------------------------------
Bismillahirrahmanirraheem
---------------------------------
🌷 ✦ La ilaha illAllah wahdahu la sharika lahu, lahul-mulk wa lahul-hamd Yuhi wa Yumeet, wa huwa Ala kulli shayin qadir
✦ *لاَ إِلَهَ إِلاَّ اللَّهُ وَحْدَهُ لاَ شَرِيكَ لَهُ لَهُ الْمُلْكُ وَلَهُ الْحَمْدُ يُحْيِي وَيُمِيتُ وَهُوَ عَلَى كُلِّ شَيْءٍ قَدِيرٌ*
✦There is no Lord except Allah , Alone with no partner, to Him belongs the dominion, and to Him is all the praise, He gives life and death, and He has power over all things
✦ : Abu Ayyub Ansari Radi Allahu Anhu narrated that: Rasool Allah Sallallahu Alaihi wasallam said: Whoever says these words ten times in the morning , for every one time Allah subhanahu will write 10 good deeds for him , Will wipe away 10 evil deeds and will raise 10 degrees for him, and these words will be equal for him as he has freed 10 captives ( if anybody say 10 times then this rewards will be ten fold) and it will be his weaopan from the beginning of the day untill the end of the day. and that day nobody will be able to do any deeds which is more better than this and if he say same words in the evening will get same rewards
Al-Silsila-tus-Sahiha-2967-Hasan
DARUSAN RAMADHAN
Darasi na Uku: Hukuncin Azumin Ramadhan
Godiya ta tabbata ga Allah Madaukakin Sarki, wanda ya halicci bayi, kuma ya shar'anta musu hukunce – hukunce da suka dace da rayuwarsu, kuma ya yi tanadin sakamako ga wanda ya kiyaye dokokinsa, da kuma alkawarin narkon azaba ga wanda ya saba masa.
Tsira da amincin Allah su tabbata ga Ma'aikin Allah, Annabi Muhammadu, da iyalan gidansa, da Sahabbansa da wadanda suka bi su da kyautatawa.
Ya ku 'yan'uwana, lallai Azumin watan Ramadhan daya ne daga cikin rukunnan Muslunci da abubuwan da aka gina shi a kansu, Allah ya ce:
{Ya ku wadanda suka yi Imani, an wajabta muku Azumi kamar yadda aka wajabta shi a kan wadanda suka gabace ku, don ku samu tsoron Allah. Ranaku ne kirgaggu, duk wanda ya kasance maras lafiya daga cikinku ko yana halin tafiya to ya kirga a wasu ranakun daban…} [al-Baqara: 183 - 184].
Annabi (saw) ya ce: ((An gina Muslunci a kan abubuwa guda biyar; Shaidawa babu abin bauta sai Allah, kuma Annabi Muhammad ma'aikin Allah ne, da tsayar da Sallah, da ba da Zakka, da aikin Hajji, da Azumin watan Ramadhan)). Sahihul Bukhari (8), Sahihu Muslim (16).
Musulmai sun yi Ijma'i a kan farlancin Azumin watan Ramadhan da kasancewarsa abu sananne wanda babu shakka a kansa a cikin Addinin Muslunci. Kuma sun yi Ijma'i yankakke babu shakka a cikinsa; duk wanda ya yi inkarin wajabcinsa to hakika ya kafirta, za a nemi ya tuba, idan ya tuba, ya yarda da wajabcin Azumin shi kenan, idan kuma ya ki tuba to za a kashe shi a matsayin kafiri, wanda ya yi ridda daga Muslunci. Ba za a yi masa wanka ba, ba za a suturce shi a likkafani ba, ba za a yi masa Sallah ba, ba za a yi masa addu'an neman rahma ba, ba za a bisne shi a makabartan Musulmai ba, kawai za a tona rami ne a can nesa a rufe shi, don kar warinsa ya dami mutane, 'yan'uwansa su cutu.
An farlanta Azumin Ramadhan ne a shekara ta biyu bayan Hijirah, don haka Manzon Allah (saw) ya yi Azumin Ramadhan na tsawon shekaru tara. Kuma farlantawan ya kasance ne a matakai guda biyu:
Na farko: an bayar da zabi tsakanin yin Azumin ko ciyarwa a madadin haka, duk da cewa; Azumin shi ya fi falala.
Mataki na biyu: wajabta Azumin Ramadhan din a kan kowa ba tare da zabi ba. Ya tabbata daga Salama dan Akwa'u (ra) ya ce: ((Lokacin da fadin Allah ya sauka: {Akwai fansan ciyar da miskini a kan wadanda za su iya yin Azumin}, sai ya kasance wanda ya ga dama sai ya sha ruwa ya biya fansa, har sai da Ayar da take bayanta ta sauka, sai ta soke ta)). Sahihul Bukhari (4507), Sahihu Muslim (1145).
Wato yana nufin fadin Allah: {Duk wanda ya halarci watan a cikinku to wajibi ne ya azumce shi. Duk wanda ya kasance maras lafiya ko yana halin tafiya to ya kirga Azumin a wasu ranakun daban}. [al-Baqarah (185)]. Sai Allah ya wajabta Azumin a kan kowa ba tare da zabi ba.
Azumin ba ya wajaba har sai an tabbatar da shigan watan Ramadhan, don haka ba a yin Azumin kafin shigan watan, saboda fadin Annabi (saw):
((Kar dayanku ya gabaci watan Ramadhan da Azumin rana daya ko biyu, sai dai idan mutum ya kasance yana yin wani Azumi na musamman to sai ya azumci ranar)). Bukhari (1914).
Ana yanke hukuncin shigan watan ne da dayan abubuwa guda biyu:
Na farko: ganin jinjirin watan Ramadhan. Allah ya ce:
{Duk wanda ya halarcin watan a cikinku to wajibi ne ya azumce shi}.
Da fadin Annabi (saw): ((Idan kun ga jinjirin watan to ku yi Azumi)). Bukhari (1907) Muslim (1080).
Ba a shardanta dole sai kowane mutum ya gani da kansa ba, a'a, idan mutumin da shaidarsa za ta tabbatar da shigan wata ya ga jinjirin watan shi kenan yin Azumin ya wajaba a kan kowa.
Amma sharadi ne wajen karban shaidar ganin watan sai mai ba da shaidar ya zama Musulmi baligi mai hankali, wanda ake yarda da maganarsa saboda yana da amana, kuma idonsa lafiya kalau yake. Amma kafiri ko yaro ko mahaukaci shigan wata ba ya tabbata da shaidarsu, saboda Hadisin Ibnu Abbas (ra) ya ce: ((Wani bakauye ya zo wajen Annabi (saw) sai ya ce: Lallai na ga jinjirin wata (yana nufin watan Ramadhan), sai Annabi (saw) ya ce: "Shin ka shaida babu abin bauta bisa cancanta sai Allah?" Sai ya ce: Eh.
Ya ce: "Ka shaida Annabi Muhammadu Manzon Allah ne?" Ya ce: Eh. Sai Annabi (saw) ya ce: "Bilal, ka sanar da mutane gobe su yi Azumi")). Abu Dawud (2340), Tirmiziy (691), Nasa'iy (2113), Ibnu Majah (1652).
Haka wanda aka san shi da karya, ko gaggawan ba da labari, ko mai raunin ido to shi ma ba a karban shaidarsa a ganin wata.
Kuma ko da mutum daya ne ya ba da shaidan ganin wata za a karba, saboda Hadisin Abdullahi dan Umar (ra) ya ce: ((Mutane sun nemi ganin jinjirin wata, sai na ba da labari wa Annabi (saw) cewa; na ganshi, sai ya dauki Azumin, kuma ya umurci mutane da su yi Azumin)). Abu Dawud (2342).
Duk wanda ya ga jinjirin wata bisa yakini to wajibi ne ya sanar da shugabannin hukuma, haka watan Shawwal ma. Saboda duk abin da sai da shi wajibi ya cika shi ma wajibi ne.
Amma idan mutum ya ganshi a wajen da yake ba zai iya sanar da shugabanni ba, to shi zai dauki Azumin, sai kuma ya yi iya kokarinsa wajen isar musu gwargwadon iyawarsa.
Idan shugabanni suka sanar da ganin wata a kafafen yada labarai to wajibi ne a yi aiki da sanarwar tasu, wajen shigan watan Ramadhan ko waninsa, saboda sanarwan hukuma hujja ne a Shari'a, ya wajaba a yi aiki da ita. Shi ya sa Annabi (saw) ya umurci Bilal da ya sanar da mutane ganin wata, bayan an tabbatar masa da ganin watan.
Kuma abin lura wajen shigan watan Ramadhan shi ne gani da ido ba lissafi ko amfani da ilimin taurari ba, kamar yadda Hadisai suka nuna cewa; da gani za a yi aiki.
Abu na biyu: ana yin hukunci da shigan watan Ramadhan da cikan watan Sha'aban kwana talatin, saboda wata ba ya wuce kwana talatin, kuma ba ya gaza kwana ishirin da tara. Don haka idan ba a samu tabbacin ganin wata a ranar ishirin da tara ba, imma saboda gajimare ko wani abin daban to sai a cika lissafin watan Sha'aban ya cika kwana talatin, bayan haka sai a yi hukunci da shigan watan Ramadhan. Annabi (saw) ya ce:
((Ku yi Azumi saboda ganin wata, ku sha ruwa (ranar Sallah) saboda ganinsa, amma idan an yi gajimare ya tare muku ganin watan to ku kirga (watan Sha'aban) ya cika kwana talatin)). Bukhari (1909), Muslim (1081).
Allah ya sa mu dace ga bin shiriya, ya ba mu albarkan da ke cikin wannan wata, ya taimake mu a kan yawaita ibada da aiyukan da'a a cikinsa, da nisantar saba masa. Allah ya ba mu tsaro da zaman lafiya a kasarmu, da sauran kasashen Musulmi gaba daya.
Dr. Aliyu Muh'd Sani
Subscribe to:
Posts (Atom)
Domin samun mustajaba a kwana 9
Khatimin Allahu Muhammadu idan ka buga adadin Allahu sau Allahu 66×66=4356 sannan sunan Muhammadu sau 92×92=8464 4356+8468=12820 Ana rubu...

-
SIRRIN MALLAKAR MUTUM MACE KO NAMIJI Amman ajitsoron Allah kada kayishi don cuta ko San zuciya ga asirigaskiyane to ga asirin kamar haka ida...