Saturday, 2 April 2022

ZAKA TSINCI JAKAR KUDI..!?



TASKAR ILLIMANTARWA:
Mal. Aminu Ibrahim Daurawa.:
SHIGA WATAN RAMADAN
ANA SHIGA WATAN RAMADAN NE TA HANYOYI GUDA BIYU, BABU TA UKU. 
Hanya ta farko: ganin jinjirin wata, shi ganin wata zai iya kasancewa ta fuskoki guda huɗu:
Mutum ɗaya tak ya ga wata shi kadai , wato babu wanda ya gani a duk garin sai shi kadai. 
Mutum biyu su gani su kadai a garin gabaɗaya, in banda su babu wanda ya gani. 
Mutane da yawa su ga wata a gari ɗaya, sauran garuruwa kuma ba a gani ba. Misali, kamar mutan gari ɗaya, ko unguwa ɗaya, ko layi ɗaya, ko yanki ɗaya, ya zamo su kadai ne suka ga wata. 
A ga wata a guraruwa daban-daban a waje daban-daban ko a qasashe daban-daban. 
Waɗannan su ne matakan da ake ganin wata ta qarqashinsu. 
Idan aka tabbatar da ganin wata ta ɗayan waɗannan matakai, shugabanni suka amince da ganin ta hanyar bin diddigi, sai a ba da sanarwar kowa ya ɗauki azumi. 
Hanya ta biyu: Idan ba a ga wata ba, wato babu wanda ya ga wata a gari, ko unguwa, ko qasa, mutum ɗaya ko biyu ko jama'a da yawa, ko kuma an sami wanda ya gani sai dai ba a yarda da ganin nasa ba. Sai a cika lissafin Sha’aban ya zamo kwana talatin (30) daidai. 
Ita wannan hanyar ba sai an tsaya neman wanda ya ga wata ba, tun da watan Sha’aban ya cika kwana talatin (30), don haka washegari sai kowa ya tashi da azumi ba sai ya jira umarnin shugaba ba. 
Don haka waɗannan su ne hanyoyin da ake shiga watan Ramadan ta cikinsu. 
     Hujjojin da suka tabbatar da hakan su ne:
Ta farko: hadisin Abdullahi Ɗan Umar رضي الله عنه inda yake cewa, Manzon Allah ﷺ ya ambaci watan Ramadan sai ya ce, “Shi dai wata kwana ashirin da tara (29) ne.” 
A wata ruwayar ya ce, “Shi wata haka ne, da haka, da haka.” sai ya haɗa 'yan yatsunsa na dama da hagu, wato yana nufin goma da goma sau biyu ashirin (20) kenan, goma ta uku kuma sai ya lanƙwashe ɗan yatsansa guda ɗaya tara kenan. A wata ruwayar kuma yana cewa, “Shi wata wani lokaci yana yin talatin (30) wani lokaci kuma yana yin ashirin da tara (29), don haka kada ku yi azumi sai kun ga wata, kada ku ajiye sai kun gan shi, idan aka yi muku lullumi, sai ku cika lissafin Sha’aban ya zama talatin (30).” () 
A ruwayar Ummu Salamah kuwa cewa ta yi, Manzon Allah ﷺ ya yi rantsuwa ba zai je wajen iyalinsa ba sai bayan wata guda, to yayin da kwana ashirin da tara (29) suka wuce, sai ya yi sammako ya shiga wajen iyalinsa da daddare, sai wadda ya shiga wajenta ta ce, ya Ma’aikin Allah ﷺ, ai ka rantse cewa ba za ka shiga wajen matanka ba, har tsawon wata guda, ya aka yi kuma ka shigo yanzu? sai ya ce, "Lallai shi wata yakan yi kwana ashirin da tara (29) ne." () 
Shi kuma hadisin Abu Bakarata رضي الله عنه da ya ruwaito daga Ma’aiki ﷺ yana cewa, “Watan Ramadan da watan zulhajji ba sa tauyewa.” () 
Abin da Malamai suka fada a kan ma’anarsa shi ne: Ishaƙ Bn Rahawaihi da Ibn Suwaidin Bn Hubairah sun ce, ma'anar ba sa tauyewa shi ne ba a tauyewa mutum ladan ayyukan da ya aikata a cikinsu ko da kuwa sun tauye a lissafi, ba za su tauye a wajen ba da ladan aiki ba. 
Shi kuma Muhammad Bn Sirina ya ce, ba za su haɗu a Shekara kowanensu ya tauye ba. 
Shi kuma Imamu Ahmad yana cewa, idan Ramadan ya tauye to Zulhajji zai cika, idan kuma Zulhajji ya tauye to Ramadan zai cika. 
Malam Alqasim Bn Muhammad ya ce, na ji Bazzaru yana cewa, waɗannan watanni biyu ba sa tauyewa a Shekara ɗaya a tare. 
An ruwaito daga Abu Hurairah رضي الله عنه ya ce, Manzon Allah ﷺ ya ce, “Ku yi azumi in kun ga wata, ku sauke in kun gan shi, idan hazo ko hadari ya rufe muku shi, ku cika kwana talatin (30) na Sha’aban.” 
A wata ruwayar ta Muslim ya ce, “In kun ga wata ku yi azumi idan kun gani ku aje, idan girjije ko hadari ya tsare ku, sai ku cika lissafin Sha’aban.” 
A wata ruwayar ta Muslim ya ce, “Ku yi azumi don ganin wata, ku ajiye don ganin wata, idan hazo ya rufe muku shi, sai ku qirga talatin (30).” () 
Haka nan hadisin Abdullahi Ɗan Abbas رضي الله عنه ya ce, Manzon Allah ﷺ yana cewa, “Kada ku gabaci wata da yin azumin kwana ɗaya ko biyu, sai dai idan akwai wani azumi da mutum ya saba yi, (sai ya dace da waɗannan ranakun) babu laifi ya yi abinsa, shi asalin wata kwana ashirin da tara ne (29).” Wannan

lafazin Abu Dawud ne.

A taqaice za mu iya cewa hanyoyin ɗaukar azumi guda huɗu ne, kamar yadda muka gabatar. 
Na farko shi ne, ganin mutum ɗaya adali, idan hukuma ta gamsu ya zama wajibi ga duk Musulmin da yake wannan garin ya ɗauki wannan azumin. 
Dalili hadisin Abdullahi Ɗan Abbas رضي الله عنه inda yake cewa, wani mazaunin qauye ya zo wajen Manzon Allah ﷺ ya ce na ga wata, sai Annabi ﷺ ya ce da shi, “Ka shaida Allah ﷻ shi kaɗai ne ba shi da abokin tarayya, kuma Annabi Muhammadu ﷺ Manzon Allah ﷻ ne? Sai mutumin ya ce eh, sai Manzon Allah ﷺ ya ce, “Ya kai Bilalu je ka ka yi shela ka sanar da mutane cewa su ɗauki azumi gobe.” () Sai dai hadisin yana da rauni, amma malamai sun yi aiki da shi. 
Abin nufi yawancin malamai da shi suke aiki cewa za a karɓi shaidar mutum ɗaya adali a gari gabaɗaya. 
Wannan shi ne ra'ayin Abdullahi Bn Mubarak, Imamus Shafi'i, da Imamu Ahmad, da Imamu Abu Hanifa, da malaman Kufa, kuma shi ne ra'ayin Jamhuru, sun qArfafi wannan da hadisin Abdullahi Ɗan Umar رضي الله عنه wanda yake cewa, mutane sun duqufa suna duban wata sai Allah ﷻ ya nuna min shi, sai na shaidawa Ma’aiki ﷺ cewa ni na ga wata, sai Ma’aiki Allahi ﷺ ya tashi da azumi kuma ya umarci mutane suka ɗauki azumin.” () 
Sai dai malam Ishak Bn Rahawaihi shi yana ganin ba za a ɗauki azumi da ganin mutum ɗaya ba, sai dai mutum biyu. 
Wannan kuma shi ne ra'ayin Imamuna Malik, da Laisu Bn Sa’ad, da Sufyanussauri, da Abdurrahman Al-Auza'i.
Allah ya karɓi ibadar mu. 
* * * *








Taskar asirai malam tv AL falaki tv Ramli da hisabi tv Mafarkinka sirrinka tv Gudun duniya tv Domin Karin bayani Sai a turo SAKO ta nombarmu ko email zamu baku amsa 👇🤳 taskaasirai@gmail.com 08124763287 08144698283

CIKAKKEN BAYANI AKAN ILIMIN TAURARI

Friday, 1 April 2022

BAYANI AKAN CIWON SUGA DA MAGANIN TA

SALLOLIN DARAREN WATAN RAMADAN

SALLOLIN DARAREN WATAN RAMADAN

BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHIM. WA SALLALLAHU ALA MUHAMMADIN WA ALI MUHAMMADIN 
.
1• Dare na Farko: Raka'a hudu Fatiha
da Qulhuwa Goma Sha biyar {15} 
Kowace Raka'a.
.

2• Dare na Biyu: Raka'a hudu Fatiha
da Inna-Anzalnahu {20} Kowace 
Raka'a. 
.
3• Dare na Uku: Raka'a {10} Fatiha da
 Qulhuwa {50} Kowace Raka'a.
.

4• Dare na Hudu: Raka'a {8} Fatiha da 
Inna-Anzalnahu {20} Kowace Raka'a.
.

5• Dare na Biyar: Raka'a {2} Fatiha da 
Qulhuwa {50} Kowace Raka'a. bayan Sallama, Allahumma Salli Ala 
Muhammadin Wa Ali Muhammadin 
{100}.
.

6• Dare na Shida: Raka'a {4} Fatiha da
 Tabara Kowace Raka'a.

.
7• Dare na Bakwai: Raka'a {4} Fatiha da Inna-Anzalnahu {13} Kowace 
Raka'a.
.

8• Dare na Takwas: Raka'a {2} Fatiha
da Qulhuwa {10} Kowace Raka'a, 
Bayan Sallama Subahanallahi {100}
.

9• Dare na Tara: Raka'a {6} Tsakanin Magriba da Isha'i, Fatiha da Kursiyyu
 {7} Kowace Raka'a. Bayan Sallama 
Salati {50}

.
10• Dare na Goma: Raka'a {20} Fatiha
da Qulhuwa {30}
.

11• Dare na Sha daya: Raka'a {2} Fatiha da Inna'a-adayna Kalkausar 
{20}.
.

12• Dare na sha biyu: Raka'a {8}
 fatiha da inna-anzalnahu {30}
Kowace Raka'a.
.

13• Dare na sha Uku: Raka'a {4} Fatiha da Qulhuwa {25} Kowace
 Raka'a.
.

14• Dare na sha Hudu: Raka'a {6} 
Fatiha da Izazul {30} Kowace Raka'a.
.

15• Dare na Sha biyar: Raka'a {4} 
Fatiha da Qulhuwa {100} Kowace Raka'a.

.
16• Dare na sha shida: Raka'a {12} 
Fatiha da Alhakumu{12} kowace
 Raka'a.
.

17• Dare na sha bakwai: Raka'a {2} 
Fatiha da Surar data samu, A Raka'a ta farko Fatiha da Qulhuwa {100}
 Bayan Sallama La'ilaha Illallahu{100}.
.

18• Dare na sha Takwas: Raka'a {4} 
Fatiha da Inna A'adayna {50} Kowace
 Raka'a.
.

19• Dare na sha Tara: Raka'a {50} Fatiha da Izazul kowace Raka'a.
.

20• Dare na 20, 21, 22, 23, da 24: A
cikin kowane dare daga wadannan
 dararen za'ayi sallah Raka'a {8} da 
abin da ya samu na daga karatu.

.
21• Dare na Ashirin da biyar: Raka'a {8} Fatiha da Qulhuwa {10} Kowace
 Raka'a.
.

22• Dare na Ashirin da Shida: Raka'a
 {8} Fatiha da Qulhuwa {10} Kowace
 Raka'a.
.

23• Dare na Ashirin da Bakwai: Raka'a {4} Fatiha da Tabara, idan ba
zaka iya ba to da Qulhuwa {25} 
Kowace Raka'a.
.

24• Dare na Ashirin da Takwas: 
Raka'a {6} Fatiha da Kursiyyu {10} da 
Qulhuwa {10} da Kawthar {10}. Bayan Sallama Salati {10}. Sallar dare
na Ashirin takwas a bisa aka same ta
a hadisai, Raka'a {6} fatiha da 
Kursiyyu {10} da Qulhuwa {10} da 
Kawthar {10}. Bayan Sallama Salati 
{100} 
.
25• Dare na Ashirin da Tara: Raka'a 
{2} Fatiha da Qulhuwa {20} Kowace 
Raka'a.
.

26• Dare na Talatin: Raka'a {12} 
Fatiha da Qulhuwa {20} Kowace 
Raka'a {8} Bayan Sallama Salati {100}. 

Yana daga cikin ayyukan dararen Watan Ramadan Yin Salla Raka'a 1000. Yadda ake yi shi ne: za ka sallaci raka'a 20 a cikin dararen ashirin na watan (wato Goman farko da Goman ta biyu). Kana mai yin raka'a takwas bayan sallar magriba
kafin sallar isha'i, sannan raka'a 12 bayan sallar isha'i. Sannan a kwanakin goman karshe za ka rika yin sallah raka'a 30, raka'a takwas bayan magariba kamar ta farko, sannan raka'a 22 bayan isha'i. idan ka lissafa zaka ga kana da 700 a cikin watan gaba daya don haka saura raka'a 300, su kuma za ka yi su ne a darare na 19 da dare na 23. Wadannan salloli za ka yi raka'a dari-dari na wannan darare ba su shafi talatin din da za ka yi a dararen ba (wato ba za ka ce tunda sallar daya ce ba, kuma na yi talatin to sai na kawo saba'in sun zama dari ke nan. A'a ba haka ba ne, za ka sallaci wadannan ashirin din na daren 19, sannan ka kawo dari. Haka ma dare na 21 da na 23 za ka yi talatin-talatin dinsu kamar yadda aka zayyana a dararen goman karshe, sannan ka kawo dari-dari ka kara. 
.
GA LISSAFIN YADDA YAKE: 
.
1● Darare Ashirin na farko da raka'a 
20×dare 20 = raka'a 400

.
2● Raka'a 30 × dare 10 = raka'a 300 
sai ka tara su 400 + 300 = 700

.
3● Raka'a 100 × 3 ) dora 19, 24, 23)
= Raka'a 300, Saika tara da 700 Zai ba ka = 700 + 300 = 1000. 
.
IDAN KUMA KA CE DORAWA ZA KA YI, TO LISSAFIN ZAI ZAMA 
.
1● Darare 20 din farko kana da
 raka'a 400
.

2● Darare 10 karshe kana da raka'a 
300
.

3● Dararen 19, 21, 23 kana da 210 
(wato idan ya zama ka dora. ne ba ka yi kowacce daban ba)

.
4● Don haka duka sun zama 400 +
300 + 210 = 910 ka ga ba su cika ba. 
.
Allah Ya sa Mu Amfana Ilaheeey.
.......copied








Tasirai malam tv AL falaki tv Ramli da hisabi tv Mafarkinka sirrinka tv Gudun duniya tv Domin Karin bayani Sai a turo SAKO ta nombarmu ko email zamu baku amsa 👇🤳 taskaasirai@gmail.com 08124763287 08144698283

Thursday, 31 March 2022

An Karɓo Daga Abi-Hurairah (ra) Yace


An Karɓo Daga Abi-Hurairah (ra) Yace: Manzon Allah (ﷺ) Yaga Wani Mutum Kwance Akan Cikinsa, Sai Yace Dashi: “Lallai Wannan Kwanciya Ce Da Allah Baya Sonta".
(Tirmizi Ya Ruwaitoshi)

A Ruwayar Bukhari Kuma Manzon Allah (ﷺ) Cewa Yayi:
(إِنَّمَا هَذِهِ ضِجْعَةُ أَهْلِ النَّارِ)

“Lallai Wannan Kwanciya Ce Ta Ƴan Wuta".

*6. RUFE ƘOFOFI DA KASHI FITILU DA KAFIN KWANCIYA BACCI:*
Yana Daga Cikin Ladubban Kwanciya Mutum Ya Rufe Ƙofar Gida da Ƙofar Ɗaki. Sannan Ka Fitilun dake Ɗakin, Sannan a Rufe Abinci da Duk Abin Sha. Hadisi Ya Tabbata Manzon Allah (ﷺ) Yana Cewa:
عَنْ جَابِرٍ قَالَ: قَالَ رَسُولُ اللَّهِ صَلَّى اللَّهُ عَلَيْهِ وَسَلَّمَ-: (أَطْفِئُوا الْمَصَابِيحَ بِاللَّيْلِ إِذَا رَقَدْتُمْ، وَغَلِّقُوا الأَبْوَابَ، وَخَمِّرُوا الطَّعَامَ وَالشَّرَابَ)
 (روا لبخاري)

An Kar6o Daga Jabir (ra) Yace: Manzon Allah (ﷺ) Yace: “Ku Kashe Fitilu Yayin da Kuka Tashi Yin Bacci. Kuma Ku Kukkule Ƙofofinku, Ku Rufe Abinci Da Abin Sha".
(Bukhari Ya Ruwaitoshi)

DAGA CIKIN LADUBBAN KWANCIYA BACCI (04)

        Da Sunan Allah Mai Rahma Mai Jinƙai

*7. YIN ADDU'OI:*
 Bayan Mutum Ya Rufe Ƙofofi da Kashe Fitilu, Ladabi Na Gama Shine Yin Addu'a Bayan Ka Kwanta ta 6angaren Jikinka Na Dama. Akwai Addu'oi Masu Yawa da Ya Tabbata Daga Manzon Allah (ﷺ) Na Karantawa. Kaɗan Daga Cikinsu Sun Haɗa da:

١. اللَّهُ لَا إِلَٰهَ إِلَّا هُوَ الْحَيُّ الْقَيُّومُ ۚ لَا تَأْخُذُهُ سِنَةٌ وَلَا نَوْمٌ ۚ لَهُ مَا فِي السَّمَاوَاتِ وَمَا فِي الْأَرْضِ ۗ مَنْ ذَا الَّذِي يَشْفَعُ عِنْدَهُ إِلَّا بِإِذْنِهِ ۚ يَعْلَمُ مَا بَيْنَ أَيْدِيهِمْ وَمَا خَلْفَهُمْ ۖ وَلَا يُحِيطُونَ بِشَيْءٍ مِنْ عِلْمِهِ إِلَّا بِمَا شَاءَ ۚ وَسِعَ كُرْسِيُّهُ السَّمَاوَاتِ وَالْأَرْضَ ۖ وَلَا يَئُودُهُ حِفْظُهُمَا ۚ وَهُوَ الْعَلِيُّ الْعَظِيمُ

٢. آمَنَ الرَّسُولُ بِمَا أُنزِلَ إِلَيْهِ مِن رَّبِّهِ وَالْمُؤْمِنُونَ ۚ كُلٌّ آمَنَ بِاللَّهِ وَمَلَائِكَتِهِ وَكُتُبِهِ وَرُسُلِهِ لَا نُفَرِّقُ بَيْنَ أَحَدٍ مِّن رُّسُلِهِ ۚ وَقَالُوا سَمِعْنَا وَأَطَعْنَا ۖ غُفْرَانَكَ رَبَّنَا وَإِلَيْكَ الْمَصِيرُ 
 ۝ (٢٨٥) لَا يُكَلِّفُ اللَّهُ نَفْسًا إِلَّا وُسْعَهَا ۚ لَهَا مَا كَسَبَتْ وَعَلَيْهَا مَا اكْتَسَبَتْ ۗ رَبَّنَا لَا تُؤَاخِذْنَا إِن نَّسِينَا أَوْ أَخْطَأْنَا ۚ رَبَّنَا وَلَا تَحْمِلْ عَلَيْنَا إِصْرًا كَمَا حَمَلْتَهُ عَلَى الَّذِينَ مِن قَبْلِنَا ۚ رَبَّنَا وَلَا تُحَمِّلْنَا مَا لَا طَاقَةَ لَنَا بِهِ ۖ وَاعْفُ عَنَّا وَاغْفِرْ لَنَا وَارْحَمْنَا ۚ أَنتَ مَوْلَانَا فَانصُرْنَا عَلَى الْقَوْمِ الْكَافِرِينَ

٣. ﺑﺴﻢ ﺍﻟﻠﻪ ﺍﻟﺮﺣﻤﻦ ﺍﻟﺮﺣﻴﻢ ﻗُﻞْ ﻫُﻮَ ﺍﻟﻠَّﻪُ ﺃَﺣَﺪٌ  ۝ ﺍﻟﻠَّﻪُ ﺍﻟﺼَّﻤَﺪُ ۝ ﻟَﻢْ ﻳَﻠِﺪْ ﻭَﻟَﻢْ ﻳُﻮﻟَﺪْ  ۝ ﻭَﻟَﻢْ ﻳَﻜُﻦْ ﻟَﻪُ ﻛُﻔُﻮًﺍ ﺃَﺣَﺪٌ ۝ 

٤. قُلْ أَعُوذُ بِرَبِّ الْفَلَقِ ۝ مِنْ شَرِّ مَا خَلَقَ ۝ وَمِنْ شَرِّ غَاسِقٍ إِذَا وَقَبَ ۝ وَمِنْ شَرِّ النَّفَّاثَاتِ فِي الْعُقَدِ ۝ وَمِنْ شَرِّ حَاسِدٍ إِذَا حَسَدَ ۝

٥. قُلْ أَعُوذُ بِرَبِّ النَّاسِ ۝ مَلِكِ النَّاسِ ۝ إِلَهِ النَّاسِ ۝ مِنْ شَرِّ الْوَسْوَاسِ الْخَنَّاسِ ۝ الَّذِي يُوَسْوِسُ فِي صُدُورِ النَّاسِ ۝ مِنَ الْجِنَّةِ وَالنَّاسِ ۝

٦. قُلْ يَا أَيُّهَا الْكَافِرُونَ ۝ لَا أَعْبُدُ مَا تَعْبُدُونَ ۝ وَلَا أَنْتُمْ عَابِدُونَ مَا أَعْبُدُ ۝ وَلَا أَنَا عَابِدٌ مَا عَبَدْتُمْ ۝ وَلَا أَنْتُمْ عَابِدُونَ مَا أَعْبُدُ ۝ لَكُمْ دِينُكُمْ وَلِيَ دِينِ ۝

٧. اللَّهُمَّ قِني عَذَابَكَ يَوْمَ تَبْعَثُ عِبَادَكَ

٨. بِاسْمِكَ اللَّهُمَّ أَمُوتُ وَأَحْيَا

٩. بِاسمِكَ رَبي وَضَعتُ جَنبِي، وبِكَ أَرفَعُهُ، إِن أَمسَكتَ نَفسِي فارحَمها وإِن أَرسَلتَها فاحفَظها بِما تَحفَظُ بِهِ عِبَادَكَ الصالِحينَ"

*8. YIN ADDU'A YAYIN FARKAWA CIKIN BACCI:*
 Mustahabi ne Idan Mutum Ya Farka Cikin Dare Yayin da Yake Bacci Ya Ambaci Ubangijinsa da Wannan Addu'ar:
(أَعُوذُ بِكَلِمَاتِ اللهِ التَّامَّةِ مِنْ غَضَبِهِ وَعِقَابِهِ ، وَشَرِّ عِبَادِهِ ، وَمَنْ هَمَزَاتِ الشَّيَاطِينِ)

“A'UZU BI KALIMÃTULLAHIT TAMMÃT MIN GHADABIHI WA IQÃBIHI, WA SHARRI IBÃDIHI, WAMIN HAMAZÃTISH SHAYÃƊIN".

ALLAH KA TSARE DAGA SHARRIN MUTUM DA ALJANI. MASU NUFIN MU DA SHARRI KA MAYAR MUSU DA SHARRINSU

سُبْحَانَكَ اللَّهُمَّ وَبِحَمْدِكَ، أَشْهَدُ أَنْ لا إِلَهَ إِلا أَنْتَ، أَسْتَغْفِرُكَ وَأَتُوبُ إِلَيْكَ











Taskar asirai malam tv AL falaki tv Ramli da hisabi tv Mafarkinka sirrinka tv Gudun duniya tv Domin Karin bayani Sai a turo SAKO ta nombarmu ko email zamu baku amsa 👇🤳 taskaasirai@gmail.com 08124763287 08144698283

Wednesday, 30 March 2022

TSARABAR RAMADAN DOMIN SAMUN KUDIN HIDIMAR AZUMI DA SALLAH

SALLAR TUBA GA ALLAH





SALLAR TUBA GA ALLAH

An ruwaito daga Abubakar Assiddeeq (RA) ya ce: Na ji Manzon Allah (SAW) yana cewa: "Babu wani bawa da zai aikata wani zunubi, sai ya kyautata alwala, sannan ya tashi ya yi sallah raka'a biyu, sai ya roki gafaran Allah face Allah ya gafarta masa, sannan ya karanta wannan Ayar: "Kuma waɗanda suke idan suka aikata wata alfãsha ko suka zãlunci kansu sai su tunã da Allah, sai su nẽmi gãfarar zunubansu ga Allah. Kuma wãne ne ke gãfara ga zunubai, fãce Allah? Kuma ba su dõge a kan abin da suka aikata ba, alhãli kuwa suna sane". 
Abu Dawud ya ruwaito, Albaniy ya ingantashi.

💦

Yana daga cikin rahamar Allah ga bayinsa bude kofar tuba a garesu wacce ba ta yankewa har sai in an zo gargarar mutuwa ko idan rana ta fito daga mafadarta.

Sababin wannan sallar shine: idan mutum ya fada cikin zunubi babba ko karama, to lallai yana wajaba a gareshi da ya gaggauta tuba ga Allah, bayan nan an so yayi wannan raka'oi guda biyu, wato mutum ya aikata wani aikin da'a don samun kusanci ga Allah, yayi tawassuli da ita ga Allah yana mai fata da kwadayin Allah ya karbi tubansa ya gafarta masa zunubansa.

●LOKACIN YIN TA:

Mustahabbi ne yin wannan sallah a lokacin da mutum yayi azamar tuba daga zunubin da ya aikata, nan take ne yayi zunubin ko kuwa an dauki lokaci da ya aikata zunubin, Ita wannan sallah an shar'anta yin ta a kowane lokaci har a lokutan da a ka hana yin nafila, saboda ita sallah ce da take da sababi, don haka an shar'anta ta duk a ka samu sababinta.

●SIFAR SALLAR TUBA

•Sallah ce nafila raka'a biyu.
•Mutum zai sallace ta shi kadai ba a jam'i ba.
•Mutum zai karanta abin da ya sawwaka mishi na daga Alkur'ani.

●Mutahabbi ne ga wanda ya tuba daga wani zunubi to ya dage da aikata ayyuka na kwarai, saboda fadin Allah:

"وَإِنِّي لَغَفَّارٌ لِّمَن تَابَ وَآمَنَ وَعَمِلَ صَالِحًا ثُمَّ اهْتَدَىٰ". (طـه :82) 

"Kuma lalle Nĩ haƙĩƙa Mai gãfara ne ga wanda ya tũba kuma ya yi ĩmãni, kuma ya aikata aikin ƙwarai, sa'an nan kuma ya nẽmi shiryuwa".

●Mafi falalar wadannan ayyuka da mai tuba zai yi shi ne: SADAKA, domin sadaka tana daga cikin manyan sabubban da suke kankare zunubai, Allah Madaukaki ya ce:

"إِن تُبْدُوا الصَّدَقَاتِ فَنِعِمَّا هِيَ ۖ وَإِن تُخْفُوهَا وَتُؤْتُوهَا الْفُقَرَاءَ فَهُوَ خَيْرٌ لَّكُمْ ۚ وَيُكَفِّرُ عَنكُم مِّن سَيِّئَاتِكُمْ ۗ وَاللَّهُ بِمَا تَعْمَلُونَ خَبِيرٌ"
(البقرة :271) 

"Idan kun bayyana sadakõki to, yana da kyau ƙwarai kuma idan kuka ɓõye su kuma kuka je da su ga matalauta, to shi ne mafi alhẽri a gareku, kuma Yana kankarẽwa daga barinku daga miyãgun ayyukanku. Kuma Allah ga abin da kuke aikatawa Masani ne".

Kuma ya tabbata a hadisin Ka'ab bn Malik (RA) cewa, a lokacin da Allah ya karba tubansa ya ce: Ya Manzon Allah yana daga cikin cikan tubana in bayar da dukiyata sadaka ga Allah da Manzonsa, sai Manzon Allah (SAW) ya ce: ka rike wani yanki na dukiyarka don alkhairi ne a gareka...". Muttafakun alaihi.

Allah ya azurtamu da yin ingantacciyar tuba, tuban da ba za mu sake komawa ga wannan zunubin ba.












Taskar asirai malam tv AL falaki tv Ramli da hisabi tv Mafarkinka sirrinka tv Gudun duniya tv Domin Karin bayani Sai a turo SAKO ta nombarmu ko email zamu baku amsa 👇🤳 taskaasirai@gmail.com 08124763287 08144698283

_MANYAN ILLOLI GUDA SHIDA NA SABAWA MAHAIFA_*


_MANYAN ILLOLI GUDA SHIDA NA SABAWA MAHAIFA_*


Hakika Annabi SAW ya yi mana umarni kamar yadda Allah da kansa yayi mana umarnin akan yin biyayya da kuma kyautata mahaifa,da kuma hani akan sabawa masu da kuma cutar dasu,sabawa mahaifa da rashin kyautata masu yana cikin mafi girma zunubai da akewa yiwa Allah anan duniya.


Annabi SAW ya baiyana mana illa da girman laifin mai sabawa Mahaifansa, ga kadan daga cikin su:-


1-ILLA TA FARKO

*Mai Cutar da mahaifansa Tsinanne ne inji Manzon Allah SAW*.


Daga Abu Hurairaita R.A yana cewa :-

"Annabi s.a.w yana cewa:-

*(La'antacce ne mai cutar da mahaifansa ko mai sabawa mahaifansa)*

@ﺍﻟﻄﺒﺮﺍﻧﻲ ﻓﻲ" ﺍﻷﻭﺳﻂ

" ‏( 8497 ‏)

@ﻭﺻﺤﺤﻪ ﺍﻷﻟﺒﺎﻧﻲ ﻓﻲ " ﺻﺤﻴﺢ ﺍﻟﺘﺮﻏﻴﺐ " ‏( 2420 ‏)


2-ILLA TA BIYU

*Allah bawa kallon mai sabawa Mahaifansa a ranar alqiyama*.


Daga Ibn Umar R.A yana cewa:-

" Manzon Allah s.a.w yace:

(Mutane guda ukku Allah bazai kallesu ba a ranar alqiyama:-

*Mai sabawa mahaifansa*

*Wanda baya kishin iyalinsa

...............)*.

@ﻭﺭﻭﻯ ﺍﻟﻨﺴﺎﺋﻲ ‏( 2562 ‏)

@ﻭﺻﺤﺤﻪ ﺍﻷﻟﺒﺎﻧﻲ ﻓﻲ " ﺻﺤﻴﺢ

ﺳﻨﻦ ﺍﻟﻨﺴﺎﺋﻲ


3-ILLA TA UKKU

*Mai sabwa mahaifa baya shiga aljanna*.


Daga Ibn Umar R.A yana cewa:-

" Manzon Allah s.a.w yace:

(..............Mutane guda ukku bazasu shiga aljanna ba a gobe alqiyama:-

*Mai sabawa mahaifansa*

*Mai kwankwadar giya*

*Mai yin gorin abinda ya bada)*. 

@ﻭﺭﻭﻯ ﺍﻟﻨﺴﺎﺋﻲ ‏( 2562 ‏)

@ﻭﺻﺤﺤﻪ ﺍﻷﻟﺒﺎﻧﻲ ﻓﻲ " ﺻﺤﻴﺢ

ﺳﻨﻦ ﺍﻟﻨﺴﺎﺋﻲ " .


4-ILLA TA HUDU

*Babu mai shiga aljanna sai wanda kasance yana biyayya ga mahaifansa kuma baya saba masu*.


Wani mutum yazo wajan Annabi s.a.w sai yace Ya Manzon Allah s.a.w:

"Na shaida babu abin bautawa bisa hakki da gaskiya sao Allah kuma kai Manzon Allah ne, kuma nayi salloli biyar na farilla,kuma na bada zakka kuma nayi azumin watan Ramada?? Sai Annabi s.a.w ya ce:

*(Wanda ya mutum akan haka yana tare da Annabawa da Shahidai Siddiqai a ranar alqiyama matuqar bai sabawa Mahaifansa ba)*

@ﻭﺭﻭﻯ ﺃﺣﻤﺪ ‏(24299 ‏)

@ﻭﺻﺤﺤﻪ ﺍﻷﻟﺒﺎﻧﻲ ﻓﻲ " ﺻﺤﻴﺢ ﺍﻟﺘﺮﻏﻴﺐ " ‏( 2515 ‏)


5-ILLA TA BIYAR

*Allah baya karbar aiyuka na mai sabawa mahaifansa inji Manzon Allah s.a.w*.


Daga Abi Umamah R.A yana cewa:

Manzon Allah s.a.w yace:

(Mutanan guda ukku Allah baya karbar aiyukan su na farilla da na nafila:-

*Mai sabawa Mahaifansa*

*Mai gorin abinda ya bayar*

*Wanda yake karyata Qaddara)*.

@ﺭﻭﺍﻩ ﺍﺑﻦ ﺃﺑﻲ ﻋﺎﺻﻢ ﻓﻲ "

ﺍﻟﺴﻨﺔ " ‏( 323 ‏) 

@ﺳﻠﺴﻠﺔ ﺍﻷﺣﺎﺩﻳﺚ ﺍﻟﺼﺤﻴﺤﺔ " ‏( 1785 ‏) ،


6-ILLA TA SHIDA

*Sabawa mahaifa yana cikin mafi giraman zunubai inji Annabi s.a.w*.


(ﺃﻻ ﺃﻧﺒﺌﻜﻢ ﺑﺄﻛﺒﺮ ﺍﻟﻜﺒﺎﺋﺮ ؟ ﻗﻠﻨﺎ : ﺑﻠﻰ ﻳﺎ ﺭﺳﻮﻝ ﺍﻟﻠﻪ ؟ ﻗﺎﻝ : ﺍﻹﺷﺮﺍﻙ ﺑﺎﻟﻠﻪ ﻭﻋﻘﻮﻕ ﺍﻟﻮﺍﻟﺪﻳﻦ . ﻭﻛﺎﻥ ﻣﺘﻜﺌﺎً ﻓﺠﻠﺲ ، ﻭﻗﺎﻝ : ﺃﻻ ﻭﻗﻮﻝ ﺍﻟﺰﻭﺭ. ﺃﻻ ﻭﺷﻬﺎﺩﺓ ﺍﻟﺰﻭﺭ ‏) ﻣﺘﻔﻖ ﻋﻠﻰ ﺻﺤﺘﻪ.


Allah ka nisantar da mu daga aikata abinda zai sanya mu sabawa Mahaifanmu.


Allah ka jikansu kamar yadda suka kulamu lokacin muna yara.


*Allah ka gafarta ma mahaifan mu baki daya*.














Taskar asirai malam tv AL falaki tv Ramli da hisabi tv Mafarkinka sirrinka tv Gudun duniya tv Domin Karin bayani Sai a turo SAKO ta nombarmu ko email zamu baku amsa 👇🤳 taskaasirai@gmail.com 08124763287 08144698283

Tuesday, 29 March 2022

*SHAN AZUMIN MAI CIKI DA MAI JEGO: RAMUWA KO CIYARWA?*

*SHAN AZUMIN MAI CIKI DA MAI JEGO: RAMUWA KO CIYARWA?*
.
.
Abu na farko da ya kamata a sani cewa, ba ya halasta ga mai ciki ko mai jego ta sha azumi don kawai tana da juna biyu ko tana shayar da jariri. Sai dai in akwai tsoron cewa azumi zai iya cutar da lafiyarta ko ya jawo mata matsala ita kanta ko danta ko kuma su duka biyun. Idan ya tabbata cewa in ta yi azumi akwai matsala, to a lokacin ne ya halasta ta sha azumi.
Malamai sun yi sabani game da hukuncin mace mai ciki ko mai jego in ta sha azumi, shin ramawa za ta yi ko ciyarwa ko kuma duka biyun? Akwai maganganu malamai kamar haka.
.
.
MAGANA TA FARKO
Abu Hanifah da Ibrahim Annakha’iy suna da ra’ayin cewa abin da ke kanta shine ramuwa kawai. Wannan kuma shine mazhabar Aliyu Dan Abu Dalib (Allah ya qara masa yarda).
MAGANA TA BIYU
In mace mai ciki ko mai shayarwa ta sha azumi saboda tana tsoron lafiyarta za ta rama ne kawai. In kuma ta sha ne saboda tsoron lafiyar danta da/ko abin da ke cikinta to za ta rama tare da ciyarwa. Wannan ita ce maganar Maliku da Sufyan da Shafi’iy da Ahmad Bn Hanbal. Hakanan kuma Al-Jassas ya hakaito irin wannan fatawa daga Abdullahi Dan Umar (Allah ya qara musu yarda) Haka nan ma Maliku ya hakaito a Muwadda daga Ibn Umar din.
 .
.
MAGANA TA UKU
In mace mai ciki ko mai shayarwa ta sha azumi abin da ke kanta shine ciyarwa kawai, babu ramuwa. Ibn Abbas (Allah ya qara musu yarda) shine ke da wannan ra’ayin cikin sahabbai. Haka nan kuma Ibn Qudamah ya hakaito irin wannan magana daga Ibn Umar (Allah ya qara musu yarda).
MAGANA TA HUDU
Mai shayarwa in ta ji tsoro saboda jaririnta to za ta sha ruwa sai ta ciyar. Mai ciki kuma in ta sha za ta rama ne; domin ta fi kama da maras lafiya. Wannan shine mazhabin Alhasan Albasariy.
 .
.
MAGANA TA BIYAR
Idan mai ciki ko mai jego ta sha azumi to ciyarwa ne akanta ba bu ramuwa, amma tana da zabin ta rama ba tare da ciyarwa ba. Wannan ita ce maganar Ishaq Dan Rahwuya.

Almubarakfuriy ya naqalto maganar Ibn Hajrin a inda yake cewa: “An yi sabani game da mai ciki da mai shayarwa da kuma wanda ya sha azumi saboda tsufa in ya sami qarshin ramawa daga baya. Shafi’iy ya ce: za su rama kuma su ciyar, Auza’iy da mutanen Kufa suka ce ramuwa ce kawai akan su banda ciyarwa”. Sa’annan ya ambaci maganganun malamai mabambamta sannan ya ce: “Abin da ya bayyana gare ni shine cewa mai ciki da mai shayarwa suna daukan hukuncin maras lafiya ne da matafiyi. Allah shine mafi sani”.

Haka nan Ibn Qudama ya hakaito maganganun malamai da hujjojin su akan mas’alar sannan ya tabbatar da cewa abin da yake ganin shine daidai shine ramuwa ce akan matar da ta ji tsoro don kan ta, da kuma ramuwa da ciyarwa a kan wacce ta ji tsoro saboda kan ta da kuma yaronta.
Ibn Bazz ya fadi cewa: “da mai ciki da mai shayarwa [in sun sha azumi] hukuncinsu shine irin hukuncin maras lafiya. Saboda haka in sun kasa yin azumi za su rama daga baya. Wasu malamai kuma sun tafi izuwa ga cewa ciyarwa za su yi, amma wannan magana ce mai rauni. Abin da yake daidai shine ramuwa ce akan su kamar yadda take kan maras lafiya da matafiyi idan sun sha azumi”. Sannan ya kara cewa: “abin da yake daidai shine mai ciki da mai jego in sun sha azumi su rama. Abin da aka ruwaito daga Ibn Abbas na cewa ciyarwa ce kawai a kansu wannan zance ne mai rauni kuma ya saba wa dalilai na shari’a…”.

A cikin fatawar majalisar qoli ta malaman kasar Saudia sun ce: “In mace mai ciki ko mai sharyarwa ta ji tsoron abin da zai faru gare ta ko ga dan ta sai ta sha azumi to ramuwa ne akan ta, hukuncin daya ne da hukuncin maras lafiya wanda ya kasa yin azumi saboda tsoron cutarwa ga kansa. Allah ya ce: (Kuma wanda daga cikinku ya kasace ba shi da lafiya ko kuma yana halin tafiya [in ya sha azumi] to ya rama adadin kwanakin da ya sha daga baya [Baqara, 185])”. Sannan suka sake cewa: “Ita kuwa mai ciki, ya wajaba akan ta tai azumi sai dai in ta ji tsoron cewa azumin zai cutar da ita ko ya cutar da abin da ke cikinta, to anan an yi mata rangwame ta sha azumi, sannan ta rama bayan ta haihu ta kuma kuma tsarkaka daga jinin biqi….











Taskar asirai malam tv AL falaki tv Ramli da hisabi tv Mafarkinka sirrinka tv Gudun duniya tv Domin Karin bayani Sai a turo SAKO ta nombarmu ko email zamu baku amsa 👇🤳 taskaasirai@gmail.com 08124763287 08144698283

KUNDIN SIRRUKAN LI'ILAFI-QURAISHIN

Domin samun mustajaba a kwana 9

 Khatimin Allahu Muhammadu  idan ka buga adadin Allahu sau Allahu 66×66=4356 sannan sunan Muhammadu sau  92×92=8464 4356+8468=12820 Ana rubu...