Wednesday, 30 March 2022
SALLAR TUBA GA ALLAH
SALLAR TUBA GA ALLAH
An ruwaito daga Abubakar Assiddeeq (RA) ya ce: Na ji Manzon Allah (SAW) yana cewa: "Babu wani bawa da zai aikata wani zunubi, sai ya kyautata alwala, sannan ya tashi ya yi sallah raka'a biyu, sai ya roki gafaran Allah face Allah ya gafarta masa, sannan ya karanta wannan Ayar: "Kuma waɗanda suke idan suka aikata wata alfãsha ko suka zãlunci kansu sai su tunã da Allah, sai su nẽmi gãfarar zunubansu ga Allah. Kuma wãne ne ke gãfara ga zunubai, fãce Allah? Kuma ba su dõge a kan abin da suka aikata ba, alhãli kuwa suna sane".
Abu Dawud ya ruwaito, Albaniy ya ingantashi.
💦
Yana daga cikin rahamar Allah ga bayinsa bude kofar tuba a garesu wacce ba ta yankewa har sai in an zo gargarar mutuwa ko idan rana ta fito daga mafadarta.
Sababin wannan sallar shine: idan mutum ya fada cikin zunubi babba ko karama, to lallai yana wajaba a gareshi da ya gaggauta tuba ga Allah, bayan nan an so yayi wannan raka'oi guda biyu, wato mutum ya aikata wani aikin da'a don samun kusanci ga Allah, yayi tawassuli da ita ga Allah yana mai fata da kwadayin Allah ya karbi tubansa ya gafarta masa zunubansa.
●LOKACIN YIN TA:
Mustahabbi ne yin wannan sallah a lokacin da mutum yayi azamar tuba daga zunubin da ya aikata, nan take ne yayi zunubin ko kuwa an dauki lokaci da ya aikata zunubin, Ita wannan sallah an shar'anta yin ta a kowane lokaci har a lokutan da a ka hana yin nafila, saboda ita sallah ce da take da sababi, don haka an shar'anta ta duk a ka samu sababinta.
●SIFAR SALLAR TUBA
•Sallah ce nafila raka'a biyu.
•Mutum zai sallace ta shi kadai ba a jam'i ba.
•Mutum zai karanta abin da ya sawwaka mishi na daga Alkur'ani.
●Mutahabbi ne ga wanda ya tuba daga wani zunubi to ya dage da aikata ayyuka na kwarai, saboda fadin Allah:
"وَإِنِّي لَغَفَّارٌ لِّمَن تَابَ وَآمَنَ وَعَمِلَ صَالِحًا ثُمَّ اهْتَدَىٰ". (طـه :82)
"Kuma lalle Nĩ haƙĩƙa Mai gãfara ne ga wanda ya tũba kuma ya yi ĩmãni, kuma ya aikata aikin ƙwarai, sa'an nan kuma ya nẽmi shiryuwa".
●Mafi falalar wadannan ayyuka da mai tuba zai yi shi ne: SADAKA, domin sadaka tana daga cikin manyan sabubban da suke kankare zunubai, Allah Madaukaki ya ce:
"إِن تُبْدُوا الصَّدَقَاتِ فَنِعِمَّا هِيَ ۖ وَإِن تُخْفُوهَا وَتُؤْتُوهَا الْفُقَرَاءَ فَهُوَ خَيْرٌ لَّكُمْ ۚ وَيُكَفِّرُ عَنكُم مِّن سَيِّئَاتِكُمْ ۗ وَاللَّهُ بِمَا تَعْمَلُونَ خَبِيرٌ"
(البقرة :271)
"Idan kun bayyana sadakõki to, yana da kyau ƙwarai kuma idan kuka ɓõye su kuma kuka je da su ga matalauta, to shi ne mafi alhẽri a gareku, kuma Yana kankarẽwa daga barinku daga miyãgun ayyukanku. Kuma Allah ga abin da kuke aikatawa Masani ne".
Kuma ya tabbata a hadisin Ka'ab bn Malik (RA) cewa, a lokacin da Allah ya karba tubansa ya ce: Ya Manzon Allah yana daga cikin cikan tubana in bayar da dukiyata sadaka ga Allah da Manzonsa, sai Manzon Allah (SAW) ya ce: ka rike wani yanki na dukiyarka don alkhairi ne a gareka...". Muttafakun alaihi.
Allah ya azurtamu da yin ingantacciyar tuba, tuban da ba za mu sake komawa ga wannan zunubin ba.
_MANYAN ILLOLI GUDA SHIDA NA SABAWA MAHAIFA_*
_MANYAN ILLOLI GUDA SHIDA NA SABAWA MAHAIFA_*
Hakika Annabi SAW ya yi mana umarni kamar yadda Allah da kansa yayi mana umarnin akan yin biyayya da kuma kyautata mahaifa,da kuma hani akan sabawa masu da kuma cutar dasu,sabawa mahaifa da rashin kyautata masu yana cikin mafi girma zunubai da akewa yiwa Allah anan duniya.
Annabi SAW ya baiyana mana illa da girman laifin mai sabawa Mahaifansa, ga kadan daga cikin su:-
1-ILLA TA FARKO
*Mai Cutar da mahaifansa Tsinanne ne inji Manzon Allah SAW*.
Daga Abu Hurairaita R.A yana cewa :-
"Annabi s.a.w yana cewa:-
*(La'antacce ne mai cutar da mahaifansa ko mai sabawa mahaifansa)*
@ﺍﻟﻄﺒﺮﺍﻧﻲ ﻓﻲ" ﺍﻷﻭﺳﻂ
" ( 8497 )
@ﻭﺻﺤﺤﻪ ﺍﻷﻟﺒﺎﻧﻲ ﻓﻲ " ﺻﺤﻴﺢ ﺍﻟﺘﺮﻏﻴﺐ " ( 2420 )
2-ILLA TA BIYU
*Allah bawa kallon mai sabawa Mahaifansa a ranar alqiyama*.
Daga Ibn Umar R.A yana cewa:-
" Manzon Allah s.a.w yace:
(Mutane guda ukku Allah bazai kallesu ba a ranar alqiyama:-
*Mai sabawa mahaifansa*
*Wanda baya kishin iyalinsa
...............)*.
@ﻭﺭﻭﻯ ﺍﻟﻨﺴﺎﺋﻲ ( 2562 )
@ﻭﺻﺤﺤﻪ ﺍﻷﻟﺒﺎﻧﻲ ﻓﻲ " ﺻﺤﻴﺢ
ﺳﻨﻦ ﺍﻟﻨﺴﺎﺋﻲ
3-ILLA TA UKKU
*Mai sabwa mahaifa baya shiga aljanna*.
Daga Ibn Umar R.A yana cewa:-
" Manzon Allah s.a.w yace:
(..............Mutane guda ukku bazasu shiga aljanna ba a gobe alqiyama:-
*Mai sabawa mahaifansa*
*Mai kwankwadar giya*
*Mai yin gorin abinda ya bada)*.
@ﻭﺭﻭﻯ ﺍﻟﻨﺴﺎﺋﻲ ( 2562 )
@ﻭﺻﺤﺤﻪ ﺍﻷﻟﺒﺎﻧﻲ ﻓﻲ " ﺻﺤﻴﺢ
ﺳﻨﻦ ﺍﻟﻨﺴﺎﺋﻲ " .
4-ILLA TA HUDU
*Babu mai shiga aljanna sai wanda kasance yana biyayya ga mahaifansa kuma baya saba masu*.
Wani mutum yazo wajan Annabi s.a.w sai yace Ya Manzon Allah s.a.w:
"Na shaida babu abin bautawa bisa hakki da gaskiya sao Allah kuma kai Manzon Allah ne, kuma nayi salloli biyar na farilla,kuma na bada zakka kuma nayi azumin watan Ramada?? Sai Annabi s.a.w ya ce:
*(Wanda ya mutum akan haka yana tare da Annabawa da Shahidai Siddiqai a ranar alqiyama matuqar bai sabawa Mahaifansa ba)*
@ﻭﺭﻭﻯ ﺃﺣﻤﺪ (24299 )
@ﻭﺻﺤﺤﻪ ﺍﻷﻟﺒﺎﻧﻲ ﻓﻲ " ﺻﺤﻴﺢ ﺍﻟﺘﺮﻏﻴﺐ " ( 2515 )
5-ILLA TA BIYAR
*Allah baya karbar aiyuka na mai sabawa mahaifansa inji Manzon Allah s.a.w*.
Daga Abi Umamah R.A yana cewa:
Manzon Allah s.a.w yace:
(Mutanan guda ukku Allah baya karbar aiyukan su na farilla da na nafila:-
*Mai sabawa Mahaifansa*
*Mai gorin abinda ya bayar*
*Wanda yake karyata Qaddara)*.
@ﺭﻭﺍﻩ ﺍﺑﻦ ﺃﺑﻲ ﻋﺎﺻﻢ ﻓﻲ "
ﺍﻟﺴﻨﺔ " ( 323 )
@ﺳﻠﺴﻠﺔ ﺍﻷﺣﺎﺩﻳﺚ ﺍﻟﺼﺤﻴﺤﺔ " ( 1785 ) ،
6-ILLA TA SHIDA
*Sabawa mahaifa yana cikin mafi giraman zunubai inji Annabi s.a.w*.
(ﺃﻻ ﺃﻧﺒﺌﻜﻢ ﺑﺄﻛﺒﺮ ﺍﻟﻜﺒﺎﺋﺮ ؟ ﻗﻠﻨﺎ : ﺑﻠﻰ ﻳﺎ ﺭﺳﻮﻝ ﺍﻟﻠﻪ ؟ ﻗﺎﻝ : ﺍﻹﺷﺮﺍﻙ ﺑﺎﻟﻠﻪ ﻭﻋﻘﻮﻕ ﺍﻟﻮﺍﻟﺪﻳﻦ . ﻭﻛﺎﻥ ﻣﺘﻜﺌﺎً ﻓﺠﻠﺲ ، ﻭﻗﺎﻝ : ﺃﻻ ﻭﻗﻮﻝ ﺍﻟﺰﻭﺭ. ﺃﻻ ﻭﺷﻬﺎﺩﺓ ﺍﻟﺰﻭﺭ ) ﻣﺘﻔﻖ ﻋﻠﻰ ﺻﺤﺘﻪ.
Allah ka nisantar da mu daga aikata abinda zai sanya mu sabawa Mahaifanmu.
Allah ka jikansu kamar yadda suka kulamu lokacin muna yara.
*Allah ka gafarta ma mahaifan mu baki daya*.
Tuesday, 29 March 2022
*SHAN AZUMIN MAI CIKI DA MAI JEGO: RAMUWA KO CIYARWA?*
*SHAN AZUMIN MAI CIKI DA MAI JEGO: RAMUWA KO CIYARWA?*
.
.
Abu na farko da ya kamata a sani cewa, ba ya halasta ga mai ciki ko mai jego ta sha azumi don kawai tana da juna biyu ko tana shayar da jariri. Sai dai in akwai tsoron cewa azumi zai iya cutar da lafiyarta ko ya jawo mata matsala ita kanta ko danta ko kuma su duka biyun. Idan ya tabbata cewa in ta yi azumi akwai matsala, to a lokacin ne ya halasta ta sha azumi.
Malamai sun yi sabani game da hukuncin mace mai ciki ko mai jego in ta sha azumi, shin ramawa za ta yi ko ciyarwa ko kuma duka biyun? Akwai maganganu malamai kamar haka.
.
.
MAGANA TA FARKO
Abu Hanifah da Ibrahim Annakha’iy suna da ra’ayin cewa abin da ke kanta shine ramuwa kawai. Wannan kuma shine mazhabar Aliyu Dan Abu Dalib (Allah ya qara masa yarda).
MAGANA TA BIYU
In mace mai ciki ko mai shayarwa ta sha azumi saboda tana tsoron lafiyarta za ta rama ne kawai. In kuma ta sha ne saboda tsoron lafiyar danta da/ko abin da ke cikinta to za ta rama tare da ciyarwa. Wannan ita ce maganar Maliku da Sufyan da Shafi’iy da Ahmad Bn Hanbal. Hakanan kuma Al-Jassas ya hakaito irin wannan fatawa daga Abdullahi Dan Umar (Allah ya qara musu yarda) Haka nan ma Maliku ya hakaito a Muwadda daga Ibn Umar din.
.
.
MAGANA TA UKU
In mace mai ciki ko mai shayarwa ta sha azumi abin da ke kanta shine ciyarwa kawai, babu ramuwa. Ibn Abbas (Allah ya qara musu yarda) shine ke da wannan ra’ayin cikin sahabbai. Haka nan kuma Ibn Qudamah ya hakaito irin wannan magana daga Ibn Umar (Allah ya qara musu yarda).
MAGANA TA HUDU
Mai shayarwa in ta ji tsoro saboda jaririnta to za ta sha ruwa sai ta ciyar. Mai ciki kuma in ta sha za ta rama ne; domin ta fi kama da maras lafiya. Wannan shine mazhabin Alhasan Albasariy.
.
.
MAGANA TA BIYAR
Idan mai ciki ko mai jego ta sha azumi to ciyarwa ne akanta ba bu ramuwa, amma tana da zabin ta rama ba tare da ciyarwa ba. Wannan ita ce maganar Ishaq Dan Rahwuya.
Almubarakfuriy ya naqalto maganar Ibn Hajrin a inda yake cewa: “An yi sabani game da mai ciki da mai shayarwa da kuma wanda ya sha azumi saboda tsufa in ya sami qarshin ramawa daga baya. Shafi’iy ya ce: za su rama kuma su ciyar, Auza’iy da mutanen Kufa suka ce ramuwa ce kawai akan su banda ciyarwa”. Sa’annan ya ambaci maganganun malamai mabambamta sannan ya ce: “Abin da ya bayyana gare ni shine cewa mai ciki da mai shayarwa suna daukan hukuncin maras lafiya ne da matafiyi. Allah shine mafi sani”.
Haka nan Ibn Qudama ya hakaito maganganun malamai da hujjojin su akan mas’alar sannan ya tabbatar da cewa abin da yake ganin shine daidai shine ramuwa ce akan matar da ta ji tsoro don kan ta, da kuma ramuwa da ciyarwa a kan wacce ta ji tsoro saboda kan ta da kuma yaronta.
Ibn Bazz ya fadi cewa: “da mai ciki da mai shayarwa [in sun sha azumi] hukuncinsu shine irin hukuncin maras lafiya. Saboda haka in sun kasa yin azumi za su rama daga baya. Wasu malamai kuma sun tafi izuwa ga cewa ciyarwa za su yi, amma wannan magana ce mai rauni. Abin da yake daidai shine ramuwa ce akan su kamar yadda take kan maras lafiya da matafiyi idan sun sha azumi”. Sannan ya kara cewa: “abin da yake daidai shine mai ciki da mai jego in sun sha azumi su rama. Abin da aka ruwaito daga Ibn Abbas na cewa ciyarwa ce kawai a kansu wannan zance ne mai rauni kuma ya saba wa dalilai na shari’a…”.
A cikin fatawar majalisar qoli ta malaman kasar Saudia sun ce: “In mace mai ciki ko mai sharyarwa ta ji tsoron abin da zai faru gare ta ko ga dan ta sai ta sha azumi to ramuwa ne akan ta, hukuncin daya ne da hukuncin maras lafiya wanda ya kasa yin azumi saboda tsoron cutarwa ga kansa. Allah ya ce: (Kuma wanda daga cikinku ya kasace ba shi da lafiya ko kuma yana halin tafiya [in ya sha azumi] to ya rama adadin kwanakin da ya sha daga baya [Baqara, 185])”. Sannan suka sake cewa: “Ita kuwa mai ciki, ya wajaba akan ta tai azumi sai dai in ta ji tsoron cewa azumin zai cutar da ita ko ya cutar da abin da ke cikinta, to anan an yi mata rangwame ta sha azumi, sannan ta rama bayan ta haihu ta kuma kuma tsarkaka daga jinin biqi….
Monday, 28 March 2022
Sunday, 27 March 2022
Saturday, 26 March 2022
Thursday, 24 March 2022
MENE NE AZUMI...?? 1. AZUMI A LUGGA
MENE NE AZUMI...??
1. AZUMI A LUGGA
Shine kamewa
2. ASHARI'ANCE:- Shine kamewa daga barin chi ko sha da saduwa da iyali tun daga ketowar alfijir har zuwa faduwar rana da niyyar yin ibada.
RUKUNAN AZUMI
1. Yin niyya
2. Kamewa dagachi ko sha da saduwa da iyali
3. Zamani (lokachin yin azumi).
SUNNONIN AZUMI
1. Gaggauta buda baki
2. Jinkirta sahur
3. Addu'a yayin buda baki
4. Yin sahur da jinkirta shi.
MAKARUHAN AZUMI
1. Kaiwa matuka wajen kurkuran baki
2. Sumba
3. Dauwamar da kallo na sha' awa
4. Tunani akan al'amuran saduwa
5. Shafa ko runguma
6. Dandanan wani abu
7. Sanya tozali
8. Yin kaho.
ABUBUWAN DA SUKE BATA AZUMI
1. Saduwan wani abu zuwa makoshi (narkakke)
2. Fitarda maniyyi ko maziyyi da gangar
3. Saduwa ta hanyar tilasta
4. Chi ko sha da tunanin sauran dare
5. Chi ko sha da gangan
6. Saduwan wani abu wanda ba narkakkeba zuwa makoshi
7. Ridda.
ABUBUWAN DA SUKE HALAS
1. Yin asiwaki
2. Sanyaya jiki da ruwa
3. Tafiya ta halas
4. Sanya magani wanda ya dache
5. Tauna wani abu ga karamin yaro
6. Sanya turare.
ABUBUWAN DA AKAYI RANGWAME
1. Hadiye yawu
2. Rinjayen amai da magwas
3. Rinjayen wani kwaro zuwa ga makoshi
4. Kuran kan hanya
5. Wayan gari da janaba
6. Yin mafarki da rana
Ya kai dan uwa mai Albarka ka taya mu yada wannan karatu/sako zaka samu lada mai yawa, domin yada ilimi yana da daga cikin Abubuwan da suke kusan ta bawa ga Mahalicci.
Taskar asirai malam tv
AL falaki tv
Ramli da hisabi tv
Mafarkinka sirrinka tv
Gudun duniya tv
Domin Karin bayani Sai a turo SAKO ta nombarmu ko email zamu baku amsa 👇🤳
taskaasirai@gmail.com
08124763287
08144698283
Wednesday, 23 March 2022
SAMUN IJABA TAKE
787
.
Aslm bayin Allah masoya annabi S, a, w,
.
Ga alkawarin sirrin samun ijaba mai qarfi sosai
.
.
Ranar lahadi ake farawa har kwana 7
.
Ana rubuta شيجكذيش kafa 777 idan aka wanke sai rubutun saika saka gaushi mai wuta acikin rubutun saika shanye take.. Saikayi wuridin.ya shaijakaziyshu.qafa 1000 to haka zakana yi zuwa kwana, 7 to wllh idai kayi hakan to insha allahu duk aikin dakayi zaka sami ijaba cikin gaggawa mujarrabun sahihun lashakka fiyhi
SIRRI
.
Aslm bayin Allah masoya annabi S, a, w,
.
Ga alkawarin sirrin samun ijaba mai qarfi sosai
.
.
Ranar lahadi ake farawa har kwana 7
.
Ana rubuta شيجكذيش kafa 777 idan aka wanke sai rubutun saika saka gaushi mai wuta acikin rubutun saika shanye take.. Saikayi wuridin.ya shaijakaziyshu.qafa 1000 to haka zakana yi zuwa kwana, 7 to wllh idai kayi hakan to insha allahu duk aikin dakayi zaka sami ijaba cikin gaggawa mujarrabun sahihun lashakka fiyhi
SIRRI
Subscribe to:
Posts (Atom)
Domin samun mustajaba a kwana 9
Khatimin Allahu Muhammadu idan ka buga adadin Allahu sau Allahu 66×66=4356 sannan sunan Muhammadu sau 92×92=8464 4356+8468=12820 Ana rubu...

-
SIRRIN MALLAKAR MUTUM MACE KO NAMIJI Amman ajitsoron Allah kada kayishi don cuta ko San zuciya ga asirigaskiyane to ga asirin kamar haka ida...